Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Takarar Sanata Adamu Aliero

bySulaiman
3 years ago
Adamu aliero

Babban Kotun Tarayya da ke zamanza a Birnin Kebbi a karkashin Jagorancin mai shari’a Baba Gana Ashigar ya tabbatar da Alhaji Haruna Saidu Dandiyo a matsayin halatacin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a karkashin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

Alhaji Haruna Saidu, wanda ya shigar da karar ya kai karar Sanata Muhammad Adamu Aliero, PDP da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) domin ya gudanar da sabon zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya, alhali bai mutu kuma ba bisa ya janye daga takarar ba.

  • Zabarmawa Sun Yi Gagarumin Taro A Kebbi

Ya kuma kai karar su kan sauya sunansa da sunan Sanata Muhammadu Adamu Aliero, wanda ya ce yana APC a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko, sabanin dokokin zaben 2022 da kundin tsarin mulkin Jam’iyyar PDP.

Yayin da yake yanke hukunci a kan karar, Mai Shari’a Baba Gana Ashigar ya yanke hukuncin

Mai shari’a Asghigar, yayin da yake gabatar da hukuncin nasa kan batutuwan da suka shafi gaba daya, ya lura cewa, ko shakka babu, a lokacin da aka gudanar da zaben fidda gwani na farko na mazabar Kebbi ta tsakiya a jam’iyyar PDP, wanda ake kara na 1 yana cikin jam’iyyar mai mulki watau APC.

Ya kuma kara da cewa, bisa ga hujojin da aka gabatar a gaban kotun, wanda ya shigar da karar ya halarci zaben fidda gwani na mazabar Kebbi ta tsakiya a zaben fidda gwani na farko, inda aka zabe shi, dan takarar Sanata na jam’iyyar PDP ya samu nasarar lashe zaben da kuri’u mafi girma yayin da wanda ake kara na 1 yana a jam’iyyar APC mai mulki a yanzu. Saboda haka, kotu ta gamsu da duk hujoji da kuma rokon da mai kara,” in ji shi.

 

A nasa martani, Lauyan mai kara, Sule O.Usman (SAN), wanda ya yaba wa Alkalin da ya gabatar da wannan hukuncin wanda ya baiwa wanda yake tsayawa damar samun nasara a Shari’ar.

A cewarsa, “Mun yi murna saboda mun tunkari Kotun da ta share Mana hawaye a fuskarmu, inda kotu ta tabbatar da Saidu Haruna Dandiyo a matsayin dan takarar kujerar Sanatan Kebbi ta tsakiya a PDP.

Lauyan wanda ake kara na daya, Barista Aminu Hassan wanda ya tsayawa I K. Sanusi SAN, wanda shi ma ya yabawa mai shari’a Baba Gana Ashigar bisa hukuncin da aka yanke kuma ya yaba da aikin da ya yi masa amma ya shaida wa manema labarai cewa, Sanata Muhammad Adamu Aliero zai daukaka kara kan hukuncin.

A nasa martani, Lauyan Hukumar INEC, Barista Ahmad Bello Mahamud ya ce sun koyi darasi da yawa a cikin hukuncin kuma ya yaba wa Mai Shari’a Ashigar bisa yanke hukunci da yayi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version