Umar Faruk">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Kotu Ta Tsare Matar Da Ake Zargi Da Sace Jariri A Kebbi

by Umar Faruk
December 3, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Kotu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A jiya ne kotun majistare mai lamba 4 da ke zamanta a Birnin-Kebbi, Babban Birnin Jihar Kebbi, a karkashin Majistare Zainab Bello Suru, ta bada umarnin cigaba da tsare Patricia Nebochi a gidan gyaran hali da ke Argungu, bayan da jami’an rundunar ‘yan sandan jihar suka cafke su ka gurfanar da ita a gaban kotun bisa tuhumar ta da aikata laifufuka biyu; laifin sace jaririn da a ka haifa a ranar 21 ga Nuwamba, 2020, da misalin karfe 4:00 na yamma a asibitin Aisha Muhammadu Buhari da ke garin Jage da kuma laifin zama sanadiyar mutuwar jaririn ta hanyar wurgar da shi.

Alkalin ta ce, za a cigaba da tsare matar ne har zuwa lokacin da za a cigaba da gabatar da shari’ar a sabuwar shekara karkashin wata babbar kotu a jihar, wacce ke da cikakken hurumin sauraron shari’ar, saboda kasancewar laifin da a ke tuhumar Patrichia, babba ne.

samndaads

Jami’in ‘yan sanda mai gabatar da karar, Sufeto Muktari Mati, ya bayyana wa Mai Shari’ar Zainab Suru cewa, “ni Sufeto Muktari Mati a madadin rundunar ‘yan sandan jihar ne ke gabatar da Patricia Nebochi, ‘yar shekaru 30 da haifuwa, wacce ke zaune a garin Tambuwal a Jihar Sakkwato, a gaban wannan kotun da laifufuka biyu.

“Laifi na farko; tuhumar ta da sace jariri sabuwar haihuwa, sai laifi na biyu na zama sanadiyyar mutuwar jaririn da wata mata mai suna Fatima Ja’afar da ke garin Galbi a karamar hukumar mulki ta Jega, wanda ya saba wa sashe na 221 da kuma na 274 na kundin tsarin hukunta masu laifi, wato Panel Cod).”

Daga nan Sufeto Mati ya nemi kotun da ta dage sauraren karar har zuwa ranar 5 ga Janairu, 2021, domin bai wa rundunar ‘yan sandan damar kammala duk binciken da su ke gudanarwa, don a dawo a ciki gaba da sauraron karar.

Bugu da kari maishari’a Zainab Bello Suru ta amince da rokon na mai gabatar da karar. Haka kuma ta bada umarnin tsare wacce a ke tuhuma a gidan gyaran hali da ke Argungu har zuwa ranar zaman shari’ar.

Sai dai kuma alkalin ta ce, wannan kotun ba ta da hurumin cigaba da sauraron karar. Don haka sai dai a jira shawarar Darakta Mai Kula da Gurfanar da Manyan Laifuka na Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kebbi, wato DPP.

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Cigaba Da Kare Cin Mutuncin Al’ummarmu A Legas, Cewar Sarki Ibrahim Goma

Next Post

Tawaga Ta Isa Minna Don Nazarin Kan Tsarin Kiwon Dabbobin Na Kasa

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Umar Faruk
24 hours ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Umar Faruk
1 day ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Umar Faruk
1 day ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Tsarin Kiwon Dabbobin

Tawaga Ta Isa Minna Don Nazarin Kan Tsarin Kiwon Dabbobin Na Kasa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version