Kotu Ta Yanke Wa Wani Matashi Dan Kasar Nijar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Laifin Kisan Kai A Kebbi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Wani Matashi Dan Kasar Nijar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Laifin Kisan Kai A Kebbi

bySulaiman and Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Wata babbar kotu ta daya da ke Birnin Kebbi, ta yanke wa wani dan kasar Jamhuriyar Nijar, Sulieman Idris, hukuncin kisa ta hanyar rataya , bisa samunsa da laifin kisan matar aure da’yar ta ‘yar shekara hudu da haihuwa a duniya.

Lauyoyin jihar sun gurfanar da Suleiman Idris a gaban kuliya tare da tuhumar shi da laifuka biyu na kisan kai wanda hukuncin kisa ne a karkashin sashe na 191 (a) da (b) na dokar Penal Code na jihar Kebbi, 2021.

  • NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a kuma Babbar jojin Jihar Sulieman Muhammad -Ambursa, ya ce masu gabatar da kara sun yi nasarar tabbatar da dukkan hujojin su da babu shakka a gaban kotu, inji kotun”

“A bisa la’akari da nauyi da shaidun da lauyoyin masu gabatar da kara su gabatar a gaban kotu, wadanda suka nuna tabbacin aikata laifin da ake tuhumar Sulieman Idris a gaban kotun sun tabbata, inji kotun”.

“ Haka Kuma bisa ga doka, tuhume-tuhume biyu na aikata laifin kisan kai da ke da hukuncin kisa a karkashin sashe na 191 (a) da (b) a karkashin dokar Penal Code, 2021 an tabbatar da su kuma wanda ake tuhumar ya nuna cewa ya aikata laifin da ake tuhumar su da aikatawa a gaban wannan kotu.

“A bisa hujojin da suka nuna aikata laifin kisa da aka tuhumi Sulieman Idris, kotu ta yanke maka hukuncin kisa bisa laifin da kotu ta kama ka da shi. Don haka kotu ta yanke maka hukuncin kisa ta hanyar rataya har sai ya mutu, inji kotu”.

“Game da roƙon neman adalci tare da jinƙai ga waɗanda ake tuhuma da lauyan nasa ya yi, kan yanke masa hukunci.

Bugu da kari, kotu ta ce” kai Sulieman Idris, an yanke maka hukuncin kisa ta hanyar rataya, kuma a rataye ka da wuya har ka mutu,inji kotun”.

Tun da farko, mai gabatar da kara, Barista Zainab muhammad- Jabbo, ta shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin da ya kashe matar har lahira tare da buga kan karamar yarinyar a kan tayal dakin mahaifiyar, wanda ya kai ga mutuwarta a ranar 11 ga Afrilu.

Ta ce bangaren da aka aikata laifukan a cikinsa ba shi da hurumi, don haka ta roki kotu da ta hukunta wadanda ake tuhuma kamar yadda yake kunshe a sashin.

A nasa jawabin, Lauyan mai kare wanda ake tuhumar, Barista Alhassan salihu-Muhammad, ya roki kotun da ta yi adalci da rahama wajen yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin daurin rai da rai, kamar yadda ya nuna nadamar matakin da ya dauka.

Mijin marigayin, Malam Akilu Aliyu, wanda ya bayyana jin dadinsa da hukuncin, ya roki gwamnatin jihar da ta gaggauta zartar da hukuncin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
2023: Akwai Yuyuwar Kwankwaso Ya Amince Ya Zama Mataimakin Peter Obi Na Jam’iyyar LP

Maganar Hadewar Kwankwaso Da Peter Obi Ta Rushe

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version