Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Cire Rubutun Ajami A Kudin Nijeriya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Cire Rubutun Ajami A Kudin Nijeriya

bySadiq
1 year ago
Ajami

Wata babbar kotun tarayya da ke Jihar Legas, ta yi watsi da wata kara da aka shigar gabanta na neman cire rubutun ajami a takardun kudin Nijeriya.

Barista Malcolm Omirhobo ne ya shigar da karar, inda yake kalubalantar Babban Bankin Nijeriya (CBN), kan kotu ta umarce shi domin cire rubutun ajami na harufan Larabci daga takardar Naira.

  • Southgate Ya Ajiye Aikin Horas Da Ingila
  • An Kaddamar Da Harkar Sada Zumunta A Tsakanin Yaran Sin Da Na Afirka

Kotun ta yi watsi da karar a ranar Talata, inda mai shari’a Yellim Bogoro, ya nuna cewa wanda ya shigar da karar ya gaza bayar da hujjoji da za su nuna cewa CBN ya sanya rubutun ajami da wata mummunar manufa.

Kafin zartar da hukuncin, kotun ta ce Nijeriya kasa ce mai cikakken ‘yanci, inda ya jaddada da cewa babu fifita wani addini ko kabila.

Tun a 2020 aka fara shari’ar, wanda sai a yau Talata babbar kotun da ke Lagos ta zartar da hukunci.

Mai shari’a Yellim, wanda ya yi watsi da karar ya kara da cewa kotun ta dogara ne da shari’ar Cif Gani Fawehinmi da Akilu da aka yi a shekarar 1998.

Kotun ta ce yayin da Cif Omirhobo ke da gurbi don sauraron kararsa amma kuma ya kasa bayar da isasshiyar hujja da za ta nuna cewa tsarin da CBN ya yi don ci gaba da amfani da rubutun ajami kan takardun Naira da rubutun Larabci, an yi shi ne da muguwar manufa.

Sauran wadanda suke cikin shari’ar sun hada da kungiyar kare hakkin Musulmi karkashin daraktanta, Farfesa Ishaq Akintola da kuma Umar Kalgo, wani fitaccen lauya mazaunin Jihar Kebbi.

Babban Daraktan kungiyar kare hakkin Musulmi , Farfesa Ishaq Akintola, bayan yanke hukuncin ya ce wannan nasara ce mai cike da albishir ga Musulmi da masoya Musulunci a fadin Nijeriya.

A martanin da ya mayar kan hukuncin, Mista Omirhobo ya ce ya nemi a ba shi kwafin hukuncin kuma zai yi nazari don daukar mataki na gaba.

Da yawa dai ba su fahimci cewa kafin zuwan turawan mulkin mallaka galibi ana amfani ne da harufan Larabci domin rubuta harsunan Afirka da ake kira “Ajami.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Kwalara Ta Hallaka Mutane 103, Mutane 3000 Sun Kamu A Nijeriya 

Kwalara Ta Hallaka Mutane 103, Mutane 3000 Sun Kamu A Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version