Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Ku Kare Kanku Daga Boko Haram – CNG Ga ’Yan Arewa

by Muhammad
November 30, 2020
in JAKAR MAGORI
2 min read
CNG
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa

Bayan kashe wasu manoma 43 da kungiyar Boko Haram ta yi a Jihar Borno, Kungiyar Hadin Gwiwar Kungiyoyin Arewa (CNG), ta yi kira ga ‘yan Arewa da su tashi tsaye su kare kansu daga Boko Haram da ‘yan fashi daga yanzu, tana mai cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da Gwamnonin Arewa sun rasa ikonsu a yankin. An kashe manoman ne a ranar Asabar a Zabarmari, da ke Karamar Hukumar Gere, yayin da masunta da dama suka ji rauni.

samndaads

Da yake magana kan lamarin a cikin wata sanarwa daga kakakinta, Abdul-Azeez Suleiman, CNG ya ce ba za a sake dogaro da sojojin gwamnati da na tarayya don kare al’ummomin Arewa ba. Kalaman nasa: “Shugaban kasa da sojojin tarayya suna ci gaba da gaya mana cewa suna yin wani abu game da tabarbarewar tsaro, amma ya zuwa yanzu duk ‘yan Arewa dole ne su fahimci cewa an yi watsi da yankinmu saboda halin da ake ciki na tayar da kayar baya wanda ke ci gaba da asarar dukiya mafi girma na Arewa; yawan jama’arta da raunana shi ta fuskar siyasa da kashe shi ta fuskar tattalin arziki.

“Ya isa daukar uzuri da alkawuran karya na aiki daga gwamnatin da har zuwa yanzu ta samu mutuncin zama mafi munin a tarihin kasarmu ta fuskar duk wani karfin da zai samar da kwarin gwiwa wajen cimma tsaron rayukan ‘yan kasa da dukiyoyinsu. “Duk ‘yan Arewa yanzu haka suna cikin fargaba game da karuwar rashin tsaro na al’ummomi da kadarorinsu a Arewa tare da karuwar hare-hare daga ‘yan fashi, barayin shanu da masu tayar da kayar baya, kawai abin da yake cewa mutanen Arewa a yanzu gaba daya suna cikin tarkon kungiyoyin ‘yan bindiga suna yawo garuruwa da kauyuka yadda suke so, suna lalata da barna.

“Mun bayyana a fili abin da ba za a yarda da shi ba ga mutanen Arewa su ci gaba da rayuwa a karkkashin wannan matakin na fadawa ga masu aikata laifuka wadanda ke kai hari, da kashe-kashe, da nakasa, da fyade, da sata, da kkona kkauyuka da shanun da aka sace, yayin da Shugaban kasa da shugabannin tsaro ke ba da barazanar da alkawuran da basu da wani tasiri. “Yanayin da duk al’ummomin Aarewa ke rayuwa a yau ba za a iya jurewa ba kuma dole ne dukkanmu mu tashi tsaye don kare kanmu tare da neman a yi garambawul nan take ga shugabannin sojojin kasar da kuma dukkanin kadarorin tsaro da doka da oda. ”

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Mazauna Ekiti Sun Kashe Dan Garkuwa Ta Hanyar Ladaka Ma Sa Duka

Next Post

Za Mu Cigaba Da Aiki Tukuru Wajen Cigaban Gezawa – Hudu Zainawa

RelatedPosts

Huhunta

Kashin Kaza Ya Makale A Huhunta Shekara 14

by Muhammad
13 hours ago
0

Wata mata ‘yar Kasar Sin mai shekara 22 da haihuwa...

Budurwarsa

Ya Kona Budurwarsa Saboda Ta Yanke Alakarsu

by Muhammad
13 hours ago
0

Wata yarinya tana cikin halin ha'ula'i na rayuwarta bayan da...

Mari

Ya Kwashe Amaryarsa Da Mari A Taron Bikinsu

by Muhammad
13 hours ago
0

Wani ango ya mari matar sa a gaban bakin da...

Next Post
Gezawa

Za Mu Cigaba Da Aiki Tukuru Wajen Cigaban Gezawa – Hudu Zainawa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version