Ku Kashe Duk Wani Dan Ta'adda Da Kuka Gani A Yankinku - Gwamnan Bauchi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Kashe Duk Wani Dan Ta’adda Da Kuka Gani A Yankinku – Gwamnan Bauchi

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad Abdulkadir, ya umarci al’ummomin fadin jihar da suke fitowa su yaki masu garkuwa da mutane da ‘yan ta’addan da suke yankunansu.

“Yau bana kunya a gaban kwamishinan ‘yansandan na ce duk wanda ya taba ku zai kashe ku, ku kashe shi. A matsayina na Babban Jami’in Tsaron jihar nan duk wanda ya taba ku kar ma ku yi wani shayi ni na ce a kashe shi.”

  • Dan Wasan Duniya, Pele, Ya Rasu Yana Da Shekaru 82
  • An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

Gwamnan, ya ce gwamnatinsa ba ta da wani mafita da ya wuce kawai ta ba da wannan umarnin domin masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga suna ci gaba da tafka ta’asarsu na kashe mazauna jihar da ba su ji basu gani ba.

Gwamnan ya ba da wannan umarnin ne biyo bayan hare-haren baya-bayan nan da aka kai wasu kauyuka tare da kashe mutane sama da 20 a karamar hukumar Alkaleri da ke jihar.

Muhammad, ya yi wannan umarnin ne a yau Alhamis yayin ziyarar kauyukan Rimi, Mansur, Yalwan Duguri dukka da suke karamar hukumar Alkaleri domin jajanta musu kan hare-haren ‘yan bindiga.

“Kuma wadannan mutanen da suka taba ku mu ma mun taba su kuma da ku muka taba su, mu ba a sanmu ragayewa ba. Duk wanda ya ce mana kule za mu ce masa cas a kasar Duguri, mun sha wahala saboda rashin rayuka da dukiya. Amma na ji dadi yadda kuka fito kuka kare hakkinku.

“Saboda haka ku fito ku yi na ranku ku fito ku yi yaki, mu ba a sanmu a ragonta ba, ba wai daga Zamfara ba, ko daga birnin Sin mutum ya fito ba za mu bar shi ba.

“Da wanda ya ke bada labari ga ‘yan bindigan nan ku fito da shi ku kawowashi wurin ‘yansanda a hukunta shi domin babu mugun mutum kamar Infoma kuma a cikinmu suke.”

A bangarensa kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan, ya shaida cewar gaggawar kai dauki ga wadanda ‘yan bindiga suka kawo hari na matukar taimakawa wajen dakile aniyar ‘yan ta’adda a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Sin Ta Fadada Samar Da Kwayoyin Ibuprofen Da Paracetamol 

Sin Ta Fadada Samar Da Kwayoyin Ibuprofen Da Paracetamol 

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version