Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar CLO Ta Karrama Gwamna Ganduje A Matsayin Gwamna Abin Koyi

by
3 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Kungiyar CLO Ta Karrama Gwamna Ganduje A Matsayin Gwamna Abin Koyi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Ya yinda jama’a ke ta kara nuna farin ciki da yadda ake ta baiwa Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje lambobin yabo daga sassa daban daban na kungiyoyin ci gaban al’umma, a wannan karon ma Gwamnan ya kara yin hafzi da wata gagarumar lambar yabon.

Wata gawurtacciyar kungiyar kare hakkin dan adama ta Cibil Liberties Organisation wadda aikinta shi ne tabbatar da gaskiya da daidaito ta karrama Gwamnan da wannan babbar lambar yabo kan kasancewar gwamna abin koyi ta fuskar yiwa al’umma hidima, musamman saboda kokarin da yake wajen ci gaban harkokin ilimi, Lafiya, samar da kayan more rayuwa, bangaren inganta harkokin shari’a, zaman lafiya da tsaro a Jihar Kano.

Da yake jawabi a lokacin taron da aka gudanar a Otal din Cubana dake Abuja, shugaban Kungiyar ,Igho Akeregha ccewa ya yi wannan shi ne tarihi tun kafuwar wannan kungiya a shekara ta 1987 wadda Jihar Kano ta tabbatar, bayan shekaru 19 da demkaradiyyar Najeriya ta kasance batare da yankewa ba, muka ga da cewar aunawa tare da yabawa wadanda suka bada gagarumar gudunmawwa ga ci gaban al’ummarsu.

Labarai Masu Nasaba

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

Ya ce a shekaru biyu da suka gabata Gwamna Ganduje ya samu nasarar  gudanar da cikakken jagoranci ta hanyar samar da tallafin inganta rayuwar Matasa da kuma farfado da harkokin tattalin arzikin Jihar Kano.

Ya ce Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje shi ne Gwamna na farko wanda wannan kungiyar ta baiwa lambar yabo, saboda haka  muke fatan zai ci gaba  isar romon demokaradiyya  ga al’ummar Jihar Kano.

Da ya ke karbar lambar yabon Mataimakin Gwamnan Kano Dakta Nasiru Yusif Gawuna wanda shine ya wakilci Gwamna Ganduje, cewa ya yi muna matukar farin cikin karbar wannan gagarumar lambar yabo daga wannan shararriyar kungiya ta CLO.

Ya ce na tsaya anan cikin karsashi domin karbar wannan babbar lambar yabo daga wannan kungiya wadda ta shahara waje tsage gaskiya  da kuma tsayawa haikan wajen yakar zalunci

Hakazalika Dakta Nasiru Yusif Gawuna ya jaddada farin cikinsa ga kungiyar CLO bisa samar  da wannan kyakkyawan tsari da zai taimakawa shugabannin wajen yin aiki tukuru domin daukaka darajar jama’ar su. Don haka sai ya tabbatarwa da Jama’a aniyar Gwamnatin Kano na hada karfi da kungiyar ta CLO don ciyar da Jihar Kano gaba, musamman yakin da take na kawar da matsalar shaye shayen miyagun kwayoyi  domin samar da nagartattun matasa a nan gaba. Kamar yadda mai Magana da yawun Mataimakin Gwamnan Kano Malam Hassan Musa Fagge ya shaidawa Jaridar LEADERSHIP A Yau.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Jan Kafa Wajen Bai Wa Kotuna Cikakken ’Yanci, Barazana Ne Ga Fanin Shari’ah

Next Post

Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Na Kokarin Sasanta Takaddamar Cinikayyarsu

Labarai Masu Nasaba

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
9 hours ago
0

...

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

Alfanun Koyon Harsunan Kasashe Ga Daliban Kimiyya – Farfesa Gwarzo

by Khalid Idris Doya
13 hours ago
0

...

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

by
19 hours ago
0

...

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

by
2 days ago
0

...

Next Post
Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Na Kokarin Sasanta Takaddamar Cinikayyarsu

Shugabannin Kasashen Sin Da Amurka Na Kokarin Sasanta Takaddamar Cinikayyarsu

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: