Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar GREKIN Za Ta Yi Tattakin Ranar Alhinin Wadanda Suka Samu Hadarin Kan Titi

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
Kungiyar GREKIN Za Ta Yi Tattakin Ranar Alhinin Wadanda Suka Samu Hadarin Kan Titi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Wata kungiya mai suna Greater Kano Initiatibe (GREKIN) ta kuduri niyyar hada tattaki na musamman, don tuna alhinin da ya faru da wadanda su ka yi hatsarurruka a kan titina.

Bayanin hakan ya fito ne a sanarwar da kungiyar ta fitar a birnin Kano, jiya Laraba, ta na mai cewa, wannan tattaki zai faru ne a ranar Lahadi, 17 ga Nuwamba, 2019, da misalin karfe 9:00 na safe, inda wurin haduwa zai kasance Gidan Sarkin Kano na Nassarawa da ke kan titi Gidan Gwamna.

A wannan tattaki ne za su rarraba takardu da za su rika tunatar da masu amfani da titina kan illolin rashin bin dokar titi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

Wannan kungiya, wacce ta hada mutane daban-daban, amma masu ra’ayin cigaban jihar Kano, an kafa ta ne wasu watanni 18 da su ka wuce, kamar yadda bayanin ya wakana.

A cikin wannan lokutan ta ce, ta yi ayyuka da dama, wadanda su ka hada da taron masu ruwa da tsaki a kan harkar shaye-shaye da ya addabi jihar Kani.

“Akwai kuma agaji da ta bayar ga wasu daga cikin wadanda su ka tsinci kansu a cikin wannan hali ta hanyar wayar mu su da kai har da ma samar mu su da sana’a,” in ji sanarwar..

Wasu daga cikin abubuwan da wannan kungiya ta kuduri niyyar bada agaji a kai ya hada da bangaren ilimi, lafiya, noma da kuma mu’amulla ta yau da kullum.

“Yanzu haka GREKIN na da mabiya fiye da 300, kuma a kullum kara samun masu ra’ayin shiga ya ke yi,” a cewar sanarwar.

Ta cigaba da cewa, “a daidai wannan gabar, akwai wani taro na gangami da GREKIN ta ke shiryawa bayan wannan tattakin, wanda za a wayar wa jama’ar Kano yadda ayyukan majalisar jiha ta ke da ire-iren hukunce-hukuncensu. Don samun karin bayani a tuntubi wannan lambar 08034656535, 07039631848, 08135917001.”

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda  Taron Zagayen Maulidi Ya Gudana A Unguwar Idi Yaraba Legas

Next Post

Kotu Ta Hana ’Yan Sanda Sake Kama Attajiri ASD Da Alkalin Kotu

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

by Abubakar Abba
13 mins ago
0

...

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

’Yan Bindigar Da Suka Sace Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Nasarawa Sun Sako Shi

by Leadership Hausa
2 hours ago
0

...

Wani Bene Ya Kuma Ruftawa Ya Danne Mutane A Legas

Wani Bene Ya Kuma Ruftawa Ya Danne Mutane A Legas

by Leadership Hausa
2 hours ago
0

...

 ‘Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 360 Da Sace 1,389 Cikin Watanni 3 A Kaduna

 ‘Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 360 Da Sace 1,389 Cikin Watanni 3 A Kaduna

by Muhammad Bashir
3 hours ago
0

...

Next Post
’Yan Sandan Sas Sun Tsare Attajiri ASD Da Alkali Kan Daurin Aure

Kotu Ta Hana ’Yan Sanda Sake Kama Attajiri ASD Da Alkalin Kotu

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: