Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Kungiyar HURIWA Ta Yi Tir Da Kama Sowore

Ta Jawo Hankalin ’Yan Sanda Kan Mutunta Dokokin Kasa

by Khalid Idris Doya
January 4, 2021
in LABARAI
2 min read
Kungiyar HURIWA Ta Yi Tir Da Kama Sowore
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kungiyar kare hakkin marubuta a Nijeriya ta (Human Rights Writers Association of Nigeria’ (HURIWA). ta nuna rashin jin dadinta wa shugaban ‘yan sandan Nijeriya Muhammad Adamu a bisa matakin ‘yan sanda na lakada dukan tsira, musgunawa da cafke mawallafin kafar Sahara Reporters Mista Omoyele Sowore a Abuja kashegarin sabuwar shekara.

A sanarwar da kungiyar ta fitar, ta shaida cewar kame Sowore wanda ke dauke da allon-tallar zanga-zangar lumana kamu ne wanda bai dace ba sam-sam, kuma ya saba wa dokokin kasa na baiwa kowa da damar zanga-zanga ta lumana.
kungiyar ta kara da cewa mai rajin gwagwarmaya domin jama’an ya fito ne domin shela kan ababen da suke tafiya ba daidai ba a kasar nan musamman kan matsalar tsaro da rashin mulki mai nagarta wanda kuma ke tafiyar da lamuran bisa lumana ba tare da wani tashin hankali ba.
HURIWA ta ce, yadda ‘yan sandan dauke da bindigogi suka musguna tare da kame Sowore da sauran masu zanga-zangar lumanar haramtacciyar kamu ce wanda hakan ya take ‘yancin walwalar dan adam tare da ‘yancin yin zanga-zangar lumana kamar yadda sashin doka 4 na kundin tsarin mulkin kasa ta 1999 ya baiwa ‘yan kasa damar yi.
kungiyar ta yi nuni da cewa, a maimakon ‘yan sandan su yi amfani da makaman hannunsu wajen yaki da ‘yan ta’adda da suka addabi shiyyar arewa maso gabas da arewa maso yamma sai suka bage da dira kan masu zanga-zangar kiran a dauki matakan gyara kan matsalolin tsaro.
“Dole ‘yan sanda su koyi yadda za su ke mutunta kwansitushin wanda ya baiwa ‘yan kasa damar kare musu kima da mutunci tare da hakkin ‘yan kasa. Abun da aka yi wa Sowore da  ‘yan tawagarsa a Gudu da ke Abuja kwata-kwata babu inda suke barazana ga tsaron kasa ko Nijeriya,”
HURIWA ta bukaci shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari da ya bada umarnin gaggawa na gaggauta sake Sowore ba tare da wani sharadi ba shi da ‘yan tawagarsa.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Fyade: Gwamnatin Ogun Ta Dakatar Da Kwamishina Bisa Zargin Keta Haddin ’Yar Shekara 16

Next Post

Gwamnati Ta Dakatar Da Fasfot Din ’Yan Nijeriya 100 Bisa Kin Zuwa Gwajin Korona

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Khalid Idris Doya
2 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Fasfot Din ’Yan Nijeriya 100 Bisa Kin Zuwa Gwajin Korona

Gwamnati Ta Dakatar Da Fasfot Din ’Yan Nijeriya 100 Bisa Kin Zuwa Gwajin Korona

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version