Umar Faruk">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Kungiyar Khadimiyya Ta Bada Tallafin Kekunan Guragu 200 Ga Musakai A Kebbi    

by Umar Faruk
January 5, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Kungiyar Khadimiyya Ta Bada Tallafin Kekunan Guragu 200 Ga Musakai A Kebbi    
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kungiyar Khadimiyya  Initiatibe for Justice and Debelopment (KIJD) a jiya ta bada tallafin kekunan guragu  guda dari biyu ga musakai a fadin kananan hukumomi 21 da ke akwai a jihar Kebbi.

Da ya ke jawabi a wurin taron bada tallafin kekunan a Birnin-Kebbi, shugaban kungiyar Khadimiyya na kasa Alhaji Malami Abdulkadir ya ce” kungiyar Khadimiyya Initiatibe for Justice and Debelopment wadda ministan Shari’a na kasa, Abubakar Chika Malami ya assasa tana son ta tabbatar da cewa dukkan musakai da ke da bukatar tallafin kekunan ko sanduna wanda ake amfani dasu wurin tafiya, wannan kungiyar ta basu tallafi a duk fadin jihar Kebbi  da ma sauran wasu jahohin kasar nan, inji shugaban kungiyar Khadimiyya na kasa Alhaji Malami Abdulkadir yayin bada tallafin ga musakai a Birnin-Kebbi a jiya”.
Shugaban ya ci gaba da cewa” kungiyar Khadimiyya Initiatibe for Justice and Debelopment kungiya cewa mai zaman kanta, wadda ke kokarin ganin cewa ta bada tallafi ga masu karamin karfi da kuma gajiyayu da marasa galihu, haka kuma tana hadin kai da kungiyoyi masu irin manufar kungiyar Khadimiyya Initiatibe for Justice and Debelopment domin cinma manufufinta da kuma samun nasarar tallafawa  al’ummar kasar nan, inji shi”. Hakazalika ya ce” wannan tallafi da aka bayar ga mutane fiye da  dari biyu a jihar Kebbi taimakon ne daga wata Cibiya maisuna Beautiful Gate Handicapped Santa da ke a jihar filato, jos da suka taimaka wurin bada wannan tallafi, inji Alhaji Malami Abdulkadir”.
Yayin da ya ke bayyana yadda za a bada tallafin, keken zamani na musakai guda 165, keke mai kacha guda 30, kujerin musakai guda 10 Sai kuma sanduna na musakai guda 20 wanda fiye da musakai dari biyu zasu ci gajiyar wannan tallafi a fadin kananan hukumomi 21 na jihar ta Kebbi, inji shugaban kungiyar Khadimiyya Initiatibe for Justice and Debelopment na kasa, Alhaji Malami Abdulkadir.
Bugu da kari ya ce” sunayen musakan da suka ci gajiyar tallafin ya fito ne daga shuwagabannin kungiyar musakai ta jihar Kebbi wanda ya kunshi kananan hukumomi 21 a jihar, domin tabbatar da adalci ga musakan.
Haka kuma ya ce, “wadannan da suka ci gajiyar tallafin sun hada da masu kasuwarci da karatun da kuma koyon sana’o’in hannu na zamani,” in ji shi.
Daga karshe shugaban kungiyar Khadimiyya Initiatibe for Justice and Debelopment ya godewa shuwagabannin kungiyar musakai ta jihar Kebbi kan irin goyon baya da suke baiwa kungiyar ga gudanar da ayyukkanta na  bada tallafi ga al’ummar.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

An Cafke Mutum Hudu Bisa Zargin Yi Wa Yara Fyade A Yobe

Next Post

Ganduje Ya Bukaci Karin Mutum 88,000 Domin Amfana Da Tallafin GEEP A Jihar Kano

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Umar Faruk
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Umar Faruk
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Umar Faruk
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post
Ganduje Ya Bukaci Karin Mutum 88,000 Domin Amfana Da Tallafin GEEP A Jihar Kano

Ganduje Ya Bukaci Karin Mutum 88,000 Domin Amfana Da Tallafin GEEP A Jihar Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version