Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Kungiyar Kutare Sun Mika Kokensu Ga Hukumar Zabe A Zamfara

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Shafi’u Saleh, Yola

A kokarin gwamnatin tarayya na inganta fannin shari’a a kasar nan, kwamishinonin harkokin shari’a daga jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja na gudanar da wani taron yini biyu a Yola, domin lalubo hanyoyin magance matsalolin da ke haifar da tashin hankali a kasar.

Da yake jawabin bude taron, Kwamishinan shari’a na kasa kuma Ministan Shari’a Abubakar Malami (SAN) yace lokaci yayi da bangaren shari’a zai mayar da hankali ga irin matsaloli da ma barazanar tashe-tashen hankulan da kasar ke fuskanta.

Yace bisa matakan da gwamnatin tarayya ke dauka shi ne na hada kwamishinonin shari’a na kasar domin tattaunawa, a matsayinsu da suke da hakkin ganin doka tayi aikinta a kasar.

Malami ya ce, “Shi ne makasudin shirya wannan taron domin a zo da wani tunani tsayayye ta yadda za a fuskanci alkibla daya a ciyar da kasa gaba, kuma a samu kwanciyar hankali da lumana”

Ya ci gaba da cewa akwai dokokin da aka tsara, taron zai duba dokar a amince da ita a mataki na tarayya a kuma nemi fahimtar sauran jihohi ta fuskan kwamishinonin shari’a, domin su amince da yin dokar da kuma rungumarta a matsayin doka.

Ya jaddada cewa; “Taron zai duba dokar a amince da ita a matakin tarayya kuma zamu nemi fahimtar jihohi a kai saboda su amince a kafa dokar kuma su yi aiki da ita a matsayin doka”.

Haka shi ma da yake jawabi a taron, gwamnan Jihar Adamawa, Umaru Bindow Jibrilla, ya yi Allah wadai da irin hare-haren da kungiyoyin matasan IPOB ke kai wa al’umman arewa mazauna yankin kudu maso gabashin kasar, yace babban abin bakin ciki ne.

Gwamnan ya cigaba da cewa matsalar rikicin Boko Haram a yankin arewa maso gabas babban misali ne na koma-bayan da rikici ke haifar wa ga kasa, “Mu da mu ka ga rikicin Boko Haram ba mu goyon bayan kowanne irin tashin hankali, saboda da haka ina mai Allah wadai da rikicin kudu maso gabashin Nijeriya”.

Gwamna Bindow ya kuma bai wa al’umman jihar musamman Igbo mazauna Jihar Adamawa tabbacin tsaro da kare lafiyarsu a irin wannan yanayin da kasar ke ciki.

SendShareTweetShare
Previous Post

Babu Wata Hanya Da Zata Bunkasa Kasuwancin Dan Adam Fiye Da Ilimi —Umar Mijinyawa

Next Post

Gwamnatin Borno Ta Baiwa ’Yan Kabilar Ibo Tabbacin Samun Cikakken Tsaro

RelatedPosts

‘Yan Ta’adda Sun Kona Ofishin ‘Yan Sanda A Inugu

‘Yan Ta’adda Sun Kona Ofishin ‘Yan Sanda A Inugu

by Sulaiman Ibrahim
57 mins ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Hankula sun kara tashi a wasu yankuna...

Dabbobi

Zamanin Kiwon Dabbobi A Sake Ya Shude – ACF

by Muhammad
8 hours ago
0

Kungiyar Ta Goyi Bayan Matsayin Gwamnonin Arewa Daga Abubakar Abba,...

Garkuwa

Neja Ce Kan Gaba Wajen Fuskantar Matsalar Masu Garkuwa Da Jama’a- Gwamna Bello  

by Muhammad
8 hours ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya...

Next Post

Gwamnatin Borno Ta Baiwa ’Yan Kabilar Ibo Tabbacin Samun Cikakken Tsaro

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version