Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aikin Kwana Uku A Kano

by
4 years ago
in LABARAI, MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kungiyar Kwadago ta kasa reshen Jihar Kano na shirin shiga yajin aikin gargadi na tsawon kwanaki  uku, Shugaban Kungiyar Kwadago na Jihar Kano Kwamared Kabiru Ado Minjibir ne ya bayyana haka alokacin taron manema labarai da kungiyar ta gudanar tare da hadin guiwar kungiyar samar da daidaito da al’amuran ma’aikata a Jihar Kano.

A cikin Jawabin na sa Kwamared Kabiru Ado Minjibir ya bukaci Gwamnatin Kano da ta dakatar da shirin da ta ke shirin farawa a watan Feburairun wannan shekara na dibar wani kaso daga cikin albashin ma’aikatan Jihar Kano a matsayin inshorar lafiya, har sai ta magance matsalolin albashi hadi da na kiwon lafiya.

Shugaban kungiyar na Jihar Kano yace akwai bukatar Gwamnati ta dakatar da shirinta na yin amfani da wasu kwararru  a tsarin biyan albashi tare da mika akalar shirin a hannun ma’aikata da suka cancanta, wanda ya yi daidai da tsarin  hukumar ma’aikata ta tarayya da kuma sauran jihohi makwabta kamar  su Jigawa da daidai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

Babban Taron LEADERSHIP: Amfani Da ‘Mashahuran Hikimomi’ Zai Warware Matsalolin Nijeriya, In JI Manyan Baki

Kwamared Kabiru Ado Minjibir yace ya lura cewa Gwamnatin Kano tana cire Naira dari uku da   saba’in da bakwai da kobo sittin (377.60) daga cikin albashin ma’aikata, da kuma a Naira dari da sittin da  takwas (168) daga bangaren ‘yan fansho ba tare gabatar da wani kwakkwaran dalili ba.

Ya ce dukkan wani kokari da muka yi a baya tun daga watan Nuwanba da disamba akan mu ga an gyara albashin ma’aikata a Jihar Kano bai samu ba, don haka daga karshe mun yanke shawarar cewar akwai tsari da gwamnatin Jihar Kano ta fito dashi na taimakekeniya kan harkar lafiya, wanda za’a fara cire kudi daga albashin ma’aikata daga wannan wata na Feburairu. Don haka mu ke kira ga gwamnati da ta dakatar da cire wadannan kudade na ma’aikata har sai, na farko an gyara albashin ma’aikata kowa ya san ma nawa ne albashin nasa kafin ya san nawa aka cirar masa, inji Kwamared Minjibir.

Har ila yau kuma Kwamare Minjibir ya bukaci Gwamnatin Kano data biya wadanda ta yiwa karin girma kudadensu dake aiki a matakin Jiha da kuma kananan hukumomi hadi da hukumar ilimin bai daya na Jihar Kano SUBEB. Ya ce lallai ne dukkan matsaloli wanda ya shafi rage albashi ko cirewa ma’aikaci wani abu, ko ma kwata-kwata mutun bai ga albashin na sa ba, ko a yanke masa wani abu ko da kuwa Naira dari biyu ce, lallai a dawowa da ma’aikata kudadensu domin hakkinsu ne.

Kwamared Minjibir ya ci gaba da cewa mun amince da cewar duka matsala ta ci gaban ma’aikata (Promotion) da kuma ci gaba na shekara shekara a kowa ne mataki ya zama wajibi a saka masu nan ba jimawa ba. Don haka zamu bi dukkan ka’idojin kungiyar kwadago ta bamu mu shiga yajin aikin jan kunne  na kwanaki uku inji, Kwamared Kabiru Minjibir.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Dan Majalisa Ya Kawo Wa Mutanen Sa Dauki A Kan Yawan Hadurran Jirgin Ruwa

Next Post

A Taimakamana Da Injinan Casa Shinkafa  A Garin Dandume

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
2 hours ago
0

...

Babban Taron LEADERSHIP: Amfani Da ‘Mashahuran Hikimomi’ Zai Warware Matsalolin Nijeriya, In JI Manyan Baki

Babban Taron LEADERSHIP: Amfani Da ‘Mashahuran Hikimomi’ Zai Warware Matsalolin Nijeriya, In JI Manyan Baki

by Bello Hamza
3 hours ago
0

...

Sanatoci

Batancin Addini: “A kafa Dokar Kiyaye Martabar Annabawa A Nijeriya”

by Sabo Ahmad
4 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
14 hours ago
0

...

Next Post

A Taimakamana Da Injinan Casa Shinkafa  A Garin Dandume

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: