Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Noman Auduga Ta Raba Irin Auduga Da Taki A Katsina

by
3 years ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kungiyar noman auduga ta kasa reshen jihar Katsina ta raba irin auduga da maganin kwari hade da takin zamani na daminar bana ga ’ya’yan kungiya 10,357 afadin jihar Katsina a karshen watan Satumba na wannan shekarar da mu ke ciki.

Wannan tabbaci ya fito ne daga bakin sakataren kungiyar na jiha, Alhaji Abdulsalam Musa Kafur.

A lokacin da wakilanmu su ka ziyarci inda a ka raba kayan ga nambobin kungiyar a Jabiri Funtua, ya iske mutanen kananan  hukomomin Faskari, Danja Funtua da karamar hukumar Bakori, su na karbar irin auduga buhu daya da buhun taki shida da maganin feshi lita takwas da fanfon feshi guda daya ga kowanne manomin auduga, wanda zai noma hekta daya ta auduga a gonarshi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Kungiyar noman auduga ta kasa reshen jihar sun raba kayan noman auduga a shiyoyi shida a fadin jihar shiyoyin sune Ingawa, Dandume, Kafur, Katsina, Funtua da shiyar Malumfashi sama da manoma 10,357 suka amfana da shirin bashin noman auduga a fadin jihar Katsina.

A binciken da wakilan mu ya gudanar yagano wasu manoma da yawan gaske anan take suke siyar da kayan da aka basu wakilanmu yazanta da wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin bashin noman audugar wadanda suka bukaci a sakaya sunayensu da kananan hukumominsu, sunkoka kwarai sunce yakamata abasu kayan tun cikin watan shida wato watan june  na kowacce shekara amma ba’a bada ba sai cikin watan tara wato satumba kenan anyi latti, shiyasa suke saida kowanne buhun takin kamfa dan buhari akan naira dubu uku kuma sun karbi bashin kowanne buhun taki akan kudi naira dubu bakwai sannan kowanne litar maganin feshi suna saidashi akan naira dari tara tara, lita takwas akan naira dubu bakwai da dari hudu N7,200 maimakon naira dubu daya dari hudu lita takwas dubu shadaya da dari hudu a yadda aka basu bashin.

Wakilanmu ya zanta da shugaban shirin na shiyar funtuwa Alhaji Hamisu malumfashi. Yace manoman zasu biya bashin a tsakanin watan farko zuwa watan ukku na sabuwar shekara mai zuwa, sakateran kungiyar na jihar katsina Alhaji Abdulsalamu Musa kafur kuma shine ko,odineta na kasa a jihohi sha daya jihohin sune Kaduna, kwara, Gombe, Adamawa, Neja, Katsina, Zamfara da sauran jihohin da ake noman auduga.

Alhaji Abdulsalam yaci gaba da cewar sama da manoman auduga dubu talatin da biyar N35, 000 suka amfana da shirin bashin noman audugar na daminar bana.

Alhaji Bature Tafoki ya yaba da shirin bashin noman audugar domin a bunkasa noma saboda tun zamanin turawa ansan yankin, Funtuwa  da malumfashi wajen noman auduga yace a jahohin arewa babu inda ake noma  auduga irin yankin Funtua a jihar Katsina da jihar Gombe zuwa Adamawa, ya ce, yakamata manoma su gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari wajen inganta kasa da abinci da kuma yaba wa shuwagabannin kungiyar noman auduga ta kasa musamman shuwagabannin kungiyar na jihar Katsina domin sunyi kokari sosai wajen taimakon membobin kungiyar ya ce babu shakka noman auduga ya inganta kuma ya karu da kashi hamsin cikin dari.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Bauchi 2019: Yau Kotu Za Ta Raba Wa Kauran Bauchi Da Barista M.A Gardama

Next Post

Sai An Bai Wa Gwamnatin Buhari Hadin Kai Za Ta Kawo Cigaba – Zakari Kuchi

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post

Sai An Bai Wa Gwamnatin Buhari Hadin Kai Za Ta Kawo Cigaba – Zakari Kuchi

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: