Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Kungiyar NURTW Ta Kaddamar Da Sabbin Shugabanni A Galma

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Balarabe Abdullahi,  Zariya

A ranar Asabar da ta gabata,kungiyar direbobin manyan motoci a karkashin kungiyar NURTW reshen karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna,ta kaddamar da sabbin shugabannin kungiyar reshen Galma,da aka zabe su a kwanakin baya.

Alhaji Kabiru Tanko, shi ne shugaban kungiyar reshen karamar hukumar Zariya, a jawabinsa a lokacin kaddamar da sabbin shugabannin, ya bukaci sabbin shugabannin da lallai ne duk abin da za su yi su bi dokokin kungiya, ya ce in wani abu kuma ya shige musu duhu,ya na shirye a kowanne lokaci ,ya ba su shawarar da za su aiwatar da ayyukansu, kamar yadda kundin tsarin mulkin kungiyar ta tsara.

A dai jawabinsa, Alhaji Kabiru ya tunatar da su cewar, sai fa sun hada kansu ne a matsayinsu na shugabanni za su sami nasarar duk wani aiki ko kuma ayyukan da suka sa a gaba da ya shafi kungiya ko kuma ciyar da membobin kungiya gaba a kowane fanni na rayuwa.

Da kuma shugaban ya juya ga membobin kungiyar, ya shawarce su da su ba wadanda suka zaba duk hadin kan da suka dace,domin su sami damar gudanar da ayyukan da aka dora ma su, da suka shafi ’ya ’yan kungiyar ko kuma wadanda kungiyar za ta yi mu’amala da su, wato direbobin manyan motoci da suke daukar kaya.

A karshen jawabinsa, Alhaji Kabiru Tanko,ya nuna matukar jin dadinsa da kuma gamsuwa na yadda mambobin kungiyar suka yi zabe ba tare da tayar da jijiyar wuya ba.Ya ce ya na fatan shugabannin kungiyar za su jagoranci kungiyar nan da shekara hudu da tsarin mulkin kungiyar ya tanadar ma su.

Shi ko sabon shugaban Alhaji Haruna Nuhu,da farko nuna godiyarsa ya yi ga Allah madaukakin sarki,da ya dora ma sa wannan nauyi na shugabancin wannan kungiya, ya ce ya na yin kira ga sauran wadanda aka zaba a mukamai daban-daban da su ba shi goyon baya, domin ya sami saukin jan ragamar kungiyar, kamar yadda dokar kungiyar ta tsara.

Da kuma ya juya ga direbobin manyan motoci da kungiyar za ta yi hulda da su, ya ce da yaddar mai duka za su shinfida adalci ga duk wani direba da ya je wannan reshe da ke Galma, sai kuma ya ce ya na fatan suma direbobin za su bi dokokin da a kungiyar ta tsara.

Sauran wadanda aka zaba sun hada da Haruna Bawa,mataimakin shugaba, sai Ya’u Musa sakatare sai Shehu Yahuza, mataimakin sakatare, sai Muntari Umar, ma’aji, sai Bashir Shehu, sakataren kudi, sai kuma Abdulhamid Magaji aka zade shi a matsayin sakataren shirye-shirye na wannan kungiya.

Sauran wadanda aka zaba sun hada da Ibrahim Hudu, mai bincike sai Kabiru Salisu,amintaccen kungiyar na daya sai Dauda Salisu amintaccen kungiyar na biyu, sai Hashimu Mohammed, jami’in ladabtar da masu laifi sai Alhaji Magaji, alkalin kungiyar, sai kuma Yusuf Tamamu, jami’in sintiri.

SendShareTweetShare
Previous Post

Iya Jajircewar Da Ka Yi APC Ta Hau Mulki Iya Wuyar Da Kake Sha Yanzu – Bishir Biro Kankia

Next Post

Wadanda Ke Zagaye Da Shugaba Buhari Ne Matsalarsa -Alhaji Mustafa

RelatedPosts

Lantarki

Gwamantin Tarayya Ta Yi Bayani Game Matsalar Karancin Wutar Lantarki A Kasar

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Ministan Wutar lantarki, Injiniya Sale Mamman,...

Direbobi

Satar Mutane A Manyan Hanyoyi: Direbobi A Zamfara Sun Tsunduma Yajin Aiki

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Direbobin abeben hawa na haya masu...

Gwamnonin

Gwamnonin Nijeriya Sun Koka Kan Tabarbarewar Tsaro

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Kungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta nuna...

Next Post

Wadanda Ke Zagaye Da Shugaba Buhari Ne Matsalarsa -Alhaji Mustafa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version