Kungiyar ‘Women Link’ Ta Wayar Da Kan Mata Sama Da 200 Kan Zaben 2023
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Women Link’ Ta Wayar Da Kan Mata Sama Da 200 Kan Zaben 2023

byAbubakar Abba
3 years ago
Women link

Gamayyar Kungiyoyin Mata a karkashin inuwar Kungiyar mata da ke fafutukar ganin an samar da shugabanci nagari a kasar nan, wato ‘Women Link For Better Gobernance’, sun yi wa shugabanin kungiyoyin mata bita domin su janyo hankalinsu a kan zaben 2023, mussaman matan Arewacin kasar kan su fito su jefa kuri’un su ga ‘yan takarar da suka cancanta a zabe mai zuwa.

A hirarta da LEADERSHIP Hausa ta yi da Mataimakiyar Shugabar gamayyar kungiyoyin kuma shugabar kungiyar da ke koyar wa mata sana’o’in hannu, Hajiya Aisha Gambo jim kadan bayan kammala taron da ya gudana a Jihar Kaduna ta bayyana cewa, “Makasudin shirya wannan taron shi ne, domin mu wayar wa mata ‘yan’uwanmu kai, musamman matan da ke a arewacin kasar nan, ganin cewa mune a kan gaba wajen fita kwanmu da kwarkwata domin jefa kuri’u a lokacin zabe, amma kuma da an ci zabe sai a barin mu a baya ba tare da an inganta rayuwarmu ba.

  • Kasar Sin Ko Da Yaushe Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Kan Batun Kasar Ukraine

“Mun wayar wa shugabanin kungiyoyin mata da ke a Jihar Kaduna kai kusan sama da 200, bisa nufin in son koma gida, su ma za su tara sauran ‘ya’yan kungiyoyin mata da suke jagoranta don su wayar masu da kai kan mahimmancin fitowar jefa kuri’un ga ‘yan takarar da suka cancanta lokacin zaben.

“Mata da dama sun yi fishi kan yadda wasu ‘yan siyasar da aka zaba a baya ba su inganta rayuwarsu, inda hakan ya sa matan suka ce sun daina fita jefa kuri’a. Shi ya sa muka hada kai domin mu wayar masu da kai da yi masu nasiha a kan mu yi hakuri mu fito mu jefa kuri’unmu ga ‘yan takarar da suka cancanta.

“Nan ba da dade wa ba, za mu sake wani sabon gangamin wayar da kan ‘yan’uwanmu mata kai wadanda za su fito daga kananan hukumomin 23 da ke a cikin jihar Kaduna kan muhimmancin jefa kuri’a a zaben 2023.”

Ta kuma yi kira ga iyayen da ke fadin kasar nan da su ja hankalin ‘ya’yansu kar su bari a yi amfani da su don yin bangar siyasa a zaben 2023.

Ita kuwa shugabar gamayyar kungiyar matan, Hajiya Maryan Yahaya Sani wacce kuma ita ce Shugabantar Gidauniyar Ummulkhairi ta ce, “Yanzu mu mata muna son mu hadu mu kafa gwamnati wacce za ta kare martabarmu da kuma ‘ya’yanmu”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
‘Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

'Yan Majalisar Wakilai Sun Bukaci Buhari Ya Yi Kokarin Kubutar Da Mutanan Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version