Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yanci Ta HURIWA Ta Shawarci Buhari: Ka Tsarkake Gwamnatinka

by
1 year ago
in LABARAI
2 min read
HURIWA
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mahdi M. Muhammad,

Kungiyar masu rajin kare ‘yancin bil’adama ta Nijeriya (HURIWA), ta yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari da ya dauki duk matakin da ya dace wajen tsarkake gwamnatin tarayya daga duk masu nuna goyon baya ga manufofin ta’addanci a kasar.

Kungiyar ta yi wannan kirar ne ga Shugaban da ya hanzarta sauke Ministan sadarwa na kasa, Isa Ali Pantami kan ayyukan da ya yi a kan kalaman da ya yi a wani faifan bidiyo da ke nuna shi a matsayin mai tausayin kungiyar ta’adda ta duniya, Al-Kaeda.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Agaji Ta Kasar Saudiyya Ta Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 131 Ga Marayu A Kebbi

Nijeriya Na Bukatar Shugaban Da Kasar Ce Kawai A Gabansa —Obasanjo

A wata sanarwa dauke da sa hannun Daraktan ta, Emmanuel Onwubiko, HURIWA ta bukaci Shugaba Buhari da ya jajirce wajen kamawa da kuma hukunta ‘yan ta’adda da ‘yan bingida irin su Fulani makiyaya masu dauke da makamai wadanda ke shirin ingiza Nijeriya cikin halin yakin basasa ta hanyar musguna wa manoma ko ina cikin kasar.

Kungiyar kare hakkin dan adam din ta kalubalanci shugaban kasar kan cewa, “ya tona asirin duk masu tausaya wa kungiyoyin ta’addanci da ke cikin gwamnatin tarayya idan har da gaske yake yi don ganin ya wargaza dukkanin kungiyoyin ta’addancin da ke Nijeriya musamman ma wadanda ke yin barazana ga cigaban kasar.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “babu yadda za a yi tunanin cewa gwamnatin da ba ta yin hakuri da ra’ayoyi mabambanta kuma ta yi matukar amfani wajen amfani da karfin ‘yan sanda dauke da makamai da sauran jami’an tsaro don murklkushe magoya bayan irin wadannan kungiyoyi masu tsautsaurar ra’ayin musulunci, wadanda suka yarda da koyarwar irin wannan ta’addancin a duniya kamar masu kirkirar kungiyoyin Jihadin Al-Kaeda na duniya.

“Abin mamaki, bayan da aka fallasa wannan mutumin kuma laifukan da ya aikata a baya suka bayyana a fili, Shugaba Muhammadu Buhari tare da duk halayensa tsarkaka ya ki yin watsi da wannan mai ikirarin mai goyon bayan kungiyar Al-Kaeda. Mai ya sa wannan gwamnatin ta yi sauri ta rarraba masu fafutukar neman-kai kamar ‘yan asalin yankin Biafra (IPOB) a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda alhali a babbar cibiyar gudanar da mulki, kasar nan na da wani wanda ko ta hanyar shigar da shi cikin gaggawa, a baya ya goyi bayan kasashen duniya ‘yan ta’adda?,” inji sanrwar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ta yaya gwamnatin Nijeriya ke son kasashe masu inganci kamar Amurka, Ingila, Ostiraliya, Kanada da Tarayyar Turai su amince da wannan gwamnatin da ke karkashinta, wanda ke ikirarin cewa yana goyon bayan koyarwar Al-Kaeda kamar Ministan Sadarwa?”

“Wannan munafurcin da aka tayar ne da iko biyu. Wajibi ne a kori Ministan Sadarwa, Sheikh Pantami ba tare da bata lokaci ba sai dai in gwamnatin Muhammadu Buhari ta yarda ta zama mai nuna goyon baya ga Al-Kaeda idan haka ne, ya kamata ‘yan Nijeriya su fito kan tituna su tilasta wa gwamnatin tarayya gaba daya na Shugaba Muhammadu Buhari ya yi murabus nan take,” inji sanarwar.

Onwubiko ya bukaci ‘yan Nijeriya da kada a yaudare su wajen amincewa da abin da ya kira ‘kalaman jinkirin nadama da Ministan ya yi wanda a baya ya yi barazanar gurfanar da wata jaridar da ta danganta shi da wasu koyarwar da ke daukaka kungiyoyin Jihadun duniya’.

Pantami ya kasance cikin labarai ne saboda dalilan da ba su dace ba a makon da ya gabata, amma kwanan nan ya fada a Abuja cewa wasu daga cikin maganganun da aka jinjina masa a baya an yi su ne bisa fahimtar da ya yi da al’amuran addini a lokacin.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

…Ta Kaure Tsakanin Goodluck Jonathan Da Babangida Aliyu

Next Post

… Dan Leken Asirin Boko Haram Ya Shiga Hannu A Yobe 

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Agaji Ta Kasar Saudiyya Ta Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 131 Ga Marayu A Kebbi

Kungiyar Agaji Ta Kasar Saudiyya Ta Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 131 Ga Marayu A Kebbi

by Umar Faruk
10 hours ago
0

...

Nijeriya Na Bukatar Shugaban Da Kasar Ce Kawai A Gabansa —Obasanjo

Nijeriya Na Bukatar Shugaban Da Kasar Ce Kawai A Gabansa —Obasanjo

by
12 hours ago
0

...

Legas: Mazauna Yankin Lekki Na Zaman Dar-Dar Kan Yuwuwar Kai Masu Hari

Legas: Mazauna Yankin Lekki Na Zaman Dar-Dar Kan Yuwuwar Kai Masu Hari

by Abubakar Abba
14 hours ago
0

...

2023: Kwamishinonin Ganduje 7 Da Ya Amince Da Ajiye Aikinsu Da Ukun Da Ya Yi Watsi Da Su

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Daliban Kwaleji 4 A Kaduna Sun Bukaci Kudin Fansa

by Abubakar Abba
14 hours ago
0

...

Next Post
Sojoji Rann

… Dan Leken Asirin Boko Haram Ya Shiga Hannu A Yobe 

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: