Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

Kurdawa Sun Jefa Kuri’ar Neman Samun ‘yancin Kai

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in KASASHEN WAJE
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kurdawan Iraki sun gudanar da kuri’ar raba gardama ta ballewa daga kasar domin samun ‘yancin kai a ranar Litinin da ta Gabata. Kurdawan sun bijerewa dukkanin wata barazana da gargadi daga Iraki da Iran da kuma Turkiya da ke adawa da matakin gudanar da kuri’ar.

Dubban Kurdawa ne suka jefa kuri’ar da za ta ba su damar ballewa daga Iraki domin samun ‘yancin gashin kai.

samndaads

Kurdawan sun yi shiga sanye da tutarsu mai launin ja da fari da kore da kuma doruwa tare da kawata unguwanni da tutar a sassan arewacin Iraki da suke fatar samun ‘yanci.

Kurdawan sun jefa kuri’ar duk da gargadi daga gwamnatin Iraki da kuma barazanar takunkumi daga Turkiya da Iran da ke makwabta da su.

Tuni dai Turkiya ta ce za ta rufe kan iyakarta da yankin na Kurdawa tare da hana su fitar da mai.

Kabilar Kurdawa ne na hudu a yawan jama’a a yankin gabas ta tsakiya kuma har yanzu ba su da wata kasa mai cin gashin kanta.

SendShareTweetShare
Previous Post

Merkel Za Ta yi Zawarcin ‘yan Jam’iyyarta

Next Post

Mai Yiwuwa Jagoran ‘Yan Adawa A Jamhuriyar Nijar Ya Koma Gida

RelatedPosts

Faduwar Trump

Me Zai Biyo Bayan Darewar Karajar Biden Da Faduwar Trump?

by Muhammad
5 days ago
0

Idanun duniya na kan ranar Larabar jiya, 20 ga Janarairu,...

Rigakafi

An Soma Yin Allurar Korona A India Da Brazil

by Muhammad
5 days ago
0

A yau asabar kasashen Duniya da suka hada Indiya ,Brazil...

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

by Muhammad
5 days ago
0

Trump ya ce mutane "ba su san aiki tukuru" da...

Next Post

Mai Yiwuwa Jagoran ‘Yan Adawa A Jamhuriyar Nijar Ya Koma Gida

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version