Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Kwalejin Kimiyya Ta Bida Ta Tantance Dalibai 120 Don Fara Karatun Digiri

by Muhammad
November 29, 2020
in LABARAI
2 min read
Kwalejin kimiyya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar

Dalibai dari da ashirin ne kwalejin kimiyya ta gwamnatin tarayya da ke Bida ta tantance dan fara karatun digiri na hadin guiwa da jami’ar kimiyya da ke Minna.

samndaads

Wannan wani cigaba ne ga dalibai dari biyar da su ka nuna bukatar fara karatun wanda yanzu haka sun yi rajista tun fara shirin a shekarar da ta gabata.

Shugaban jami’ar da ya samu wakilcin darakta mai kula hadakar kwasakwasai na jami’ar,  Farfesa Johnson Olusegun Oyefo, ya bayyana hakan a lokacin bukin tantance daliban a babban dakin karatu na Twin Theatre a kwalejin.

Ya jawo hankalin daliban da kar su jefa kan su a harkokin rashin gaskiya a lokacin jarabawa, da kuma wasu miyagun halaye wanda ya sabawa dokokin makarantar, da su zauna lafiya da kowa a cikin makarantar.

A bayanisa, shugaban Poly Bida, Dakta Abubakar Abdul Dzukogi, wanda mataimakinsa a bangaren gudanarwa ya wakilce shi, Dakta Sani Man-Yahaya, ya baiwa sabbin daliban tabbacin za a samu lokacin koyarwa da ilmantarwa wadatacce.

Ya nemi daliban da su yi anfani da wannan damar na samar da shirin dan su cin ma burinsu na kasancewa masu anfani ga kasa da duniya baki daya.

Darakta mai kula da hadakar kwasakwasai na kwalejin, Dakta Ndako Yahaya, ya yabawa nasarar da aka samu tsakanin kwalejin da jami’ar kimiyyar kan wannan shirin, inda ya bayyana shugaban kwalejin a matsayin mai kwazo da kokarin ganin an samu nasara akan shirin.

Yace duk da matsalolin da kwalejin ke fuskanta, kwalejin na yaye dalibai da dama sabanin wasu makarantu da ke hadin guiwa kan kwasakwasai da jami’ar.

Wasu daliban da muka zanta da su, sun nuna jin dadinsu akan yadda shugabannin kwalejin ke samar da kwasakwasan da kwalejin ba ta da su daga wasu jami’o’i musamman darussan digiri dan anfanar al’umma bisa jagorancin shugaban kwalejin. Inda suka baiwa dalibai yan uwansu shawara su zama masu bin doka da oda da kauracewa duk wani abinda zai janyo tashin hankali a kwalejin, dan ganin sun kammala karatun su akan lokaci da samun sakamako mai kyau.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ya Kamata A Kawar Da Kwadayi Don Tabbatar Da Adalci

Next Post

Ina Farin Ciki Da Inganta Rayuwar Matasa Sama Da 50,000—Dakta Yahaya Danjuma

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post
Rayuwar Matasa

Ina Farin Ciki Da Inganta Rayuwar Matasa Sama Da 50,000—Dakta Yahaya Danjuma

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version