Kwamandan Yaki Da 'Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamandan Yaki Da ‘Yan Sara-Suka Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Zamfara

byAbubakar Abba
2 years ago
Suka

Kwamandan kungiyar da ke yaki da ‘yan sara-suka na Jihar Zamfara, Bello Bakyasuwa, ya tsallake harin ‘yan bindiga a lokacin da yake kan hanyarsa zuwa Jihar Kaduna daga Gusau, babban birinin jihar Zamfara.

A cikin sanarwar da aka sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai a yau Talata, Bakyasuwa ya bayyana cewa, ‘yan bindigar dauke da muggan makamai, sun kai masa harin a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Zariya da maraicen ranar Alhamis din da ta gabata.

  • Zazzabin Lassa Ya Yi Ajalin Mutum 154 A Nijeriya —NCDC
  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Bakyasuwa wanda tsohon soja ne, ya ci gaba da cewa, “Na tsallake harin ‘yan bindigar kwanaki hudu lokacin ina kan hanyar Kaduna zuwa Funtua daga Zariya.”

Ya kara da cewa, “A yanzu haka, ina kwace a gadon asibiti, rayuwata na cikin hatsari, ina fuskantar yawan kai min hari da nake zargin wasu ‘yan bindiga ne, ke daukar nauyi. ”

Bakyasuwa ya kuma jaddada cewa, harin ya auku a kan sa ne, lokacin da yake kan hanyarsa daga Gusau zuwa Kaduna a cikin motarsa kirar Hilux, inda ya ce, ya lura da wasu motocin Hilux biyu da kuma wata motar kirar BMW na binsa a baya.

Kwamandan ya bayyana cewa, “Ganin cewa, hankali ba bai nutsu da motocin da ke bina a baya ba, sai na tsaya a wajen duba ababen hawa da ke a Yankara, inda motocin suka wuce.”

A cewarsa, “Daga nan, na ci gaba da tafiyata bayan na wuce garin Funtua da misalin karfe 8:30 na daren ranar, na lura da mota kirar Hilux da mota kirar BMW na bi na a baya, inda motar ta BMW ta shiga gabana ta kuma tilasta min tsayawa akan hanyar.”

Ya bayyana cewa,” Wadanda ke a cikin motar sai kwai suka fara bude wa motar da nake ciki wuta, inda muka shafe awanni muna yin musayar wuta da su. ”

Ya ce, “Na yi tsalle daga cikin mota ta, inda hakan ya janyo na samu raunuka a fuskata na kuma yi targade a kafata.”

Bakyasuwa ya ci gaba da cewa, ”’Yan bindigar wadanda aka yo hayarsu sun ci gaba da harbi, amma na samu nasarar tsallake wa na shiga wani daji jini na zuba daga jikina.”

Ya ce, ya ci sa a ‘yansanda sun iso wajen bayan sun ji harbin bindiga, inda suka yi gaggawar kubutar da ni suka kuma kaini asibiti.

Ya ce, “Bayan an duba ni a asibitin na kwana a kauyen da safe direbana ya zo kauyen ya sauke ni zuwa Kaduna don a duba lafiyata sosai. ”

Bakyasuwa ya bayyana cewa, motarsa ta lalace sosai biyo bayan ta sha ruwan albarusai, inda ya koka da cewa, ko a ‘yan watannin baya, wasu ‘yan bindiga sun kai wa direbansa hari a garin Gusau lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa unguwar Gwaza zuwa Gusau, inda suka kwace motarsa.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su kawo masa dauki, domin rayuwarsa na a cikin hatsari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

Mai Tsaron Minista Ya Bindige Mai Gidansa A Uganda 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version