Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Kwamishinan Ilimin Jihar Kano Ya Jinjina Wa Daliban Firamare Da Kungiyar KISS

by Rabiu Ali Indabawa
February 2, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Kwamishinan Ilimin Jihar Kano Ya Jinjina Wa Daliban Firamare Da Kungiyar KISS
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kwamishinan ilimi na jihar Kano Alhaji Sanusi Sa’idu Kiru, Majidadin Kiru ya lashi takobin ganin duk wani dan jihar Kano ya samu ingantaccen ilimi, yayi wannan kira ne a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a santocin da daliban firamare ke rubuta jarabawar tafiya Sakandire ne a fadin jihar ta Kano.

Kwamishinan ilimin ya kara da tambayar daliban ko da me son ya tafi sekandire ta kwana wato boarding school a turance, yayin da su kuma daliban mafiya yawanci maza ne suka daga hannayensu sama wanda yake nuna alamar sun amince za su tafi makarantun kwana, a cikin muryar ta barkwanci Mai girma kwamishinan ya ce wato ku ‘yan mata kun fi son aure ke nan ko?, yayin da suka ba shi amsa da cewa Baba ilimin yara mata shine a kan gaba, kwamishinan yayi dariya ya ce musu gwamnatin Babanmu Ganduje ta mike tsaye tsayin daka domin ganin ta samar muku ingantacce ilimi a jihar mu ta Kano mai albarka, ba ma iya makarantar firamare ko Sekandire ba har ma da makarantun gaba da sakandire.
Mai girma kwamishinan ilimin ya rufe taron da kara godewa dalibai, malamai da ma’aikatan ilimin jihar Kano da suka shirya jarabawar shiga makarantar gaba da Firamare wacce aka fi sani da sunan Common Entrance Edamination kuma a nuna gamsuwar sa akan yadda aka gudanar da jarabawar.
A bangare guda kuma Kwamishinan bai tsaya a nan ba har sai da yakarbi bakuncin matasa ‘yan wasan kwallon kafa ta kiru Soccer Stars United wacce aka fi sani da suna KISS.
kungiyar kwallon kafar ta Kiru Soccer Star ta kawo masa ziyarar ban girma ne domin nuna goyon bayan su da yadda Kwamishinan ilimin jihar ta kano ya jijirce domin ganin matasa maza da mata sun samu ci gaba ta fuskar ilimi da harkokin wasanni a jihar, kungiyar dai ta samu jagorancin shuwagabannin ta kamar irin su Koci-kocin kungiyar, inda Koci Sa’idu wanda akafi sani da suna Rambo ya jangoranci tawagar.
A jawabinsa shi wanda ya samu damar jagorancin ziyarar wato Koci Rambo, ya jaddada godiyar su da goyon bayan da Kwamishinan Ilimi na jihar Kano ke bai wa matasa domin ci gaban wasanni a jihar Kano kuma ya kara da cewa suna matukar mika godiyar su ga kwamishin domin gudunmuwar da ya basu ta rigunan kwallon kafa da aka fi sani da suna Jessy a turance da kuma kwallayen kafa da aka fi sani da suna ball a turance, kuma sun ci alwashin ba shi gudunmuwa domin ganin Jihar Kano ta cigaba.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Boko Haram Ta Kashe Biyu, Ta Sace ’Yan Sanda Yayin Ziyarar Sabbin Manyan Hafsoshi

Next Post

Katsinawa Da Dama Za Su Amfana Da Tallafi Daga Gwamnatin Tarayya – Girka

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Rabiu Ali Indabawa
5 days ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Rabiu Ali Indabawa
5 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Rabiu Ali Indabawa
5 days ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Gwamnatin Katsina

Katsinawa Da Dama Za Su Amfana Da Tallafi Daga Gwamnatin Tarayya – Girka

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version