Daga Wakilinmu.
A ranar Larabar da ta gabata ne Kwamitin Tallafatawa Marayu na Abuja karkashin jagorancin Sheikh Saidu Musa Yelwa na Kungiyar Izala wato JIBWIS ta raba wa ‘yan gudun hijira dake sansanoni daban-daban a yankin Abuja shinkafa fiye da buhuna 500.
Shinkafar wadda wani bawan Allah ya kawo a matsayin gudumawarsa ga dubban ‘yan gudun hijirar da rigingimu su ka raba da muhallansu dake fama da wahalhalun rayuwa, an sauke su a Babban Masallacin Juma’a na Shelkwatar Kungiyar Izala dake Utako a birnin tarayya Abuja.
Babban Limamin Masallacin, Imam Abdullahi Umar Adam ne ya jagoranci kwamitin zuwa rabon shinkafar ga ‘yan gudun hijirar da suka hada da Apo, Wasaa, Durmi, Waru, Maleshiya Estate Apo Billege da sauransu, inda daruruwan ‘yan gudun hijirar ke rarrabe a kwangwaye da bacoci mafi yawansu mata da yara kanana.
Haka kuma malamin ya kara da cewa, wannan wani bangare ne na shirin Kungiyar Izala don tallafawa marayu da ‘yan gudun hijiran, wadda kimanin wata guda kenan mu ka gabatar da irin wannan tallafi a wannan masallaci ga daruruwan marayu da mabukata. Sannan sai ya yi kira ga Attajirai da su rika yin koyi da irin wadannan bayin Allah wajen tallafawa mabukata a fadin kasar nan, musamman ma marayu, zawarawa da ‘yan gudun hijira.