Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Kwamitin Marayun Abuja Ta Raba Shinkafa buhu 500 Ga ‘Yan Gudun Hijira

by Tayo Adelaja
July 27, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Wakilinmu.

A ranar Larabar da ta gabata ne Kwamitin Tallafatawa Marayu na Abuja karkashin jagorancin Sheikh Saidu Musa Yelwa na Kungiyar Izala wato JIBWIS ta raba wa ‘yan gudun hijira dake sansanoni daban-daban a yankin Abuja shinkafa fiye da buhuna 500.

Shinkafar wadda wani bawan Allah ya kawo a matsayin gudumawarsa ga dubban ‘yan gudun hijirar da rigingimu su ka raba da muhallansu dake fama da wahalhalun rayuwa, an sauke su a Babban Masallacin Juma’a  na Shelkwatar Kungiyar Izala dake Utako a birnin tarayya Abuja.

Babban Limamin Masallacin, Imam Abdullahi Umar Adam ne ya jagoranci kwamitin zuwa rabon shinkafar ga ‘yan gudun hijirar da suka hada da Apo, Wasaa, Durmi, Waru, Maleshiya Estate Apo Billege da sauransu, inda daruruwan ‘yan gudun hijirar ke rarrabe a kwangwaye da bacoci mafi yawansu mata da yara kanana.

A yayin da yake zantawa da wakilinmu, Imam Abdullahi Umar ya bayyana cewa wannan wata sadaka ce da wani bawan Allah ya aiko, inda ya bukaci a mika ta ga ‘yan gudun hijira wadanda ya ce ya samu labarin irin wahalar da su ke fama da ita. “Wannan wata sadaka ce da wani bawan Allah ya aiko, don a rabawa ‘yan gudun hijirar da suke nan kewayen Abuja, kuma ba wannan ne karon farko da ya aiko irin wannan tallafi ba, a bara ma ya aiko da cikin tirela guda, sannan ya ce amana ce a garemu da mu sada ta zuwa ga wadannan bayin Allah dake cikin bukatu. A yau kamar yadda ku ke gani mun raba sama da buhuna 300, sannan kuma gobe idan Allah Ya kaimu zamu karasa ragowar rabon ga mabukatan,” a cewarsa.

Haka kuma malamin ya kara da cewa, wannan wani bangare ne na shirin Kungiyar Izala don tallafawa marayu da ‘yan gudun hijiran, wadda kimanin wata guda kenan mu ka gabatar da irin wannan tallafi a wannan masallaci ga daruruwan marayu da mabukata. Sannan sai ya yi kira ga Attajirai da su rika yin koyi da irin wadannan bayin Allah wajen tallafawa mabukata a fadin kasar nan, musamman ma marayu, zawarawa da ‘yan gudun hijira.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Majalisa Ta Rattaba Hannu Kan Takardar Amincewa Wanzarda Jami’an ‘Peace Corp’c

Next Post

Mun Kwato Naira Biliyan 329 Daga Kamfanonin Mai- EFCC

RelatedPosts

Jam’iyyar APC Ta Raba Tallafin Kayan Azumi Na Sama Da Naira Biliyan Daya A Zamfara

by Daurawa Daurawa
2 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara, karkashin...

Taho-mu-gama Kan Shugabancin PDP A Kano

Taho-mu-gama Kan Shugabancin PDP A Kano

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Yusuf Shu’aibu   Abin Da Ya Sa Tambuwal Yake...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yadda Za A Kawo Karshen Ta’addanci A Arewa Maso Yamma — Gwamna Ganduje

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhamad Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje...

Next Post

Mun Kwato Naira Biliyan 329 Daga Kamfanonin Mai- EFCC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version