Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturola-Janar Na NIS Ya Amince Da Nadin Tony Akuneme A Matsayin Sabon Kakakin Hukumar Na Kasa

bySadiq
3 years ago
NIS

Babban Kwanturolan Hukumar Shige da Fice ta Kasa, Isah Jere Idris, ya amince da nadin Tony Akuneme, mataimakin Kwanturolan Shige da Fice (DCI), a matsayin sabon kakakin hukumar.

Nadin nasa na dauke ne cikin wata sanarwa da kakakin sashen ayyuka, CSI KS Kure, ya fitar a ranar Laraba.

  • Subul Da Bakan Tinubu: Alamu Ne Na Ba Zai Iya Shugabancin Nijeriya Ba- Dino Melaye
  • Kotu Ta Kori Karar Da Maina Ya Shigar Kan Ministan Harkokin Cikin Gida Da Wasu

Ya maye gurbin DCI Amos Okpu wanda ya yi ritaya bayan shafe shekaru 35 yana yi wa kasa hidima.

DCI Akuneme, dan asalin Jihar Imo ne. Ya yi Digirinsa na farko a Falsafa a Jami’ar Fatakwal, da ke Jihar Ribas.

Ya kuma yi digirin digirgir a fannin shari’a na kasa da kasa a Jami’ar Legas da Difloma a aikin jarida.

Ya halarci kwasa-kwasai daban-daban a ciki da wajen kasar nan; ciki har da babban kwas na Sufiritanda a makarantar horon shige da fice da ke Kano.

DCI Akuneme ya yi aiki da sashen hulda da jama’a na NIS na tsawon shekaru 29 a fannin tsaron kan iyaka da gudanarwa.

A tsawon shekarun aikinsa a NIS, ya yi aiki a fannoni daban-daban.

Ya yi aiki tukuru a sashen kula da jama’ar, a 2015 ya yi aiki a ofishin karamin ministan Ilimi a matsayin Mataimaki na Musamman akan Yada Labarai har zuwa 2019.

A baya ya yi ayyuka daban-daban a gida da wajen kasar nan.

Ya kasance mataimakin kakakin shiyyar A, da ke Legas daga 1995 zuwa 2005, kakakin hukumar a Jihar Akwa Ibom daga 2005 zuwa 2008, mataimakin kakaki daga 2008 zuwa 2011 sannan ya rike mukamin babban jami’i a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Kasar Kanada daga 2011 zuwa 2014.

Har zuwa lokacin nadinsa a baya-bayan nan, ya kasance Shugaban sashen hukumar da ke kula da ayyukan ‘yan Nijeriya da ke kasashen waje.

Tuni DCI Akuneme ya kama aiki a matsayin sabon kakakin Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
2023: Za A Fara Shirye-shiryen Aikin Hajji Ranar 21 Ga Disamba – NAHCON

2023: Za A Fara Shirye-shiryen Aikin Hajji Ranar 21 Ga Disamba – NAHCON

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version