Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

byUmar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa (NCS) a Jihar Kebbi, ta kama wasu kayayyakin fasa kwauri da kudinsu ya kai Naira miliyan 78.6 a watan Oktoban 2022 a jihar.

Shugaban hukumar Kwastam, Mista Joseph Attah ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a kan ayyukan hukumar na watan Oktoba a Birnin Kebbi.

  • Shugaba Xi Zai Gabatar Da Jawabi A Yayin Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 5
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Fa’ida A Zahiri Ga Jama’ar Afirka

Ya ce rundunar ta samu nasarori a cikin muhimman ayyukan da suka shafi aikin dakile fasa kwauri, ta samar da kudaden shiga da kuma saukaka kasuwanci.

A cewarsa: “An ci gaba da samun karuwar kudaden shiga na hukumar. A tsawon lokacin da ake bitar, mun samar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 162.2 a matsayin kudaden shiga daga harajin shigo da kayayyaki. Wannan shi ne mafi girma tun bayan bude iyakar ta Kamba da ke a Jihar ta Kebbi.

“Rundunar ta kuma taimaka wajen fitar da kayayyakin da ake sarrafa su a cikin gida na sama da Naira biliyan 2 a daidai lokacin da ake gudanar da bincike,” in ji Attah.

Ya ce, rundunar ta umurci jami’ansu da su kara sanya ido a cikin lungu da sako na lungu da sako na ruwa a kokarinsu na dakile ayyukan fasa-kwauri a cikin lungu da sako na jihar.

“Saboda haka, kokarin da aka yi ya haifar da kama wasu kayayyaki iri-iri har 16 da suka hada da, fakiti 284 na kwamfutar tafi-da-gidanka, tabar wi-wi, motoci 4 da aka yi amfani da su, wadanda kuma akwai Motocin na shi ga jama’a kirar Honda guda biyu da aka yi amfani da su, da motar dizal guda daya da kuma babbar motar tifa.

“Sauran sun hada da, bale 139 na tufafin hannu, buhunan shinkafa 345 na kasar waje (kowanne kilogiram 50), lita 2,250 na man fetur (PMS), kwali 38 na man shafawa (bleaching cream), guda 80 na batura masu amfani da hasken rana, da dai sauransu.

“Abin da ake tsamani da za a biya na harajin kayayyakin da aka kama ya kai Naira miliyan 78.6,” inji shi.

Kazalika, Mista Attah ya bayyana kudurin rundunar na tabbatar da cewa wadanda suka zabi shigo da kaya ko fitar da su ta iyakar Kamba, sai bin ka’idojin da suka dace na dokar kasa.

“Za ku yarda da ni, cewa yayin da sauran kayayyakin da aka kama na da kididdigar kudi, ba za mu iya kididdige yawan barnar da kwayoyi masu hadari da sauran abubuwa ke haifarwa a cikin al’umma ba.”

Bugu da kari ya ce “Irin wannan abu idan aka fito da shi a cikin al’umma yana taimaka wa dukkan manyan laifukan da muke gani a cikin al’ummarmu.

“Za a mika tabar wi-wi ga hukumar NDLEA jihar Kebbi domin daukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Daga karshe dai, mista Joseph Attah ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da aikin da aka ba su na dakile ayyukan fasa kwaurin ba tare da kasawa ba duk da kalubalen da ake fuskanta daga ‘yan kasa masu taimaka wa ga aikata miyagun laifuka a kan jami’ansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

An Kashe 'Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version