Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kwaya Ce Ta Kashe Budurwar Da Aka Samu A Masaukin Bakin Yobe – ’Yan Sanda

by
1 year ago
in LABARAI
1 min read
Kwaya Ce Ta Kashe Budurwar Da Aka Samu A Masaukin Bakin Yobe – ’Yan Sanda
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

A sanarwar da rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ke jihar Yobe, ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya nuna shan miyagun kwayoyi ne ya yi sanadin mutuwar budurwa nan yar shekaru 18, wadda aka tsinci gawarta a masaukin bakin gwamnatin jihar da ke birnin Damaturu a mako da ya gabata.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar a jihar Yobe, ASP Dungus Abdul-Kareem shi ne ya bayyana hakan a ranar Talata, wanda ya kara da cewa, binciken nasu ya tabbatar da cewa matashiyar- Bilkisu Ali, ta mutu ne sakamakon kwayoyin da ta sha fiye da kima.

Bugu da kari kuma, tun a ranar 7 ga Janairun 2021 rundunar ‘yan sandan ta kama Al-bash Yahaya Ibrahim tare da wasu mutum uki wadanda take zargi da laifin kisan budurwar.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Al’amarin da ya jawo ci gaba da tsare wadanda ake zargin tare da ajiye gawar matashiyar asibiti har lokacin da aka kammala binciken abinda ya yi sanadin mutuwarta.

ASP Dungus ya kara da cewa, rundunar ‘yan sandan za ta mika wadannan mutum hudu da ake zargin a gaban kotu domin amsa tuhume-tuhumen da ake musu wadanda su ka hada da zargin hada baki wajen aikata laifin kashe budurwar da aikata zina.

A hannu guda kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ta gargadi jama’a su guji yada jita-jita maras tushe wadanda za su jawo rudani ga yan uwa da makusantan marigayiyar kana barazana ga tsaro a jihar.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Abinda Ya Sa Hon. Bello Kumo Ya Ciri Tuta A Siyasar Gombe

Next Post

Boko Haram Ta Rasa Inda Za Ta Saka Kanta A Borno – NAF

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
7 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
9 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
Maboyar ‘Yan Ta’adda

Boko Haram Ta Rasa Inda Za Ta Saka Kanta A Borno – NAF

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: