Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno

byAbubakar Sulaiman
7 months ago
Bukar

Wani malami a Jihar Borno, mai suna Hassan Bukar, ya koka kan yadda ya shafe watanni 20 yana aiki ba tare da albashi ba saboda zargin rashin halartar aiki na mako uku. Bukar, malamin Turanci a Makarantar Sakandare ta GSS Damasak, ya bayyana cewa bai halarci aiki ba ne saboda yana kula da matarsa da ke jinya a asibiti.

Duk da cewa ya rubuta wasiƙun neman afuwa kuma ya koma bakin aiki, har yanzu ba a mayar masa da albashinsa ba. Ya ce shugaban makarantar, Alhaji Shettima Ali, ya wanke shi daga zargin guduwa daga aiki kuma ya yaba da ƙoƙarinsa, amma har yanzu gwamnati ba ta mayar masa da albashinsa ba.

  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno

WikkiTimes ta ruwaito cewa, Bukar ya ce ya sanar da Kwamishinan Ilimi na Jihar Borno game da matsalarsa yayin da ya ziyarci makarantar, inda aka yi alƙawarin shawo kan matsalar. Sai dai duk da an gayyace shi zuwa ofishin kwamishinan, an hana shi shiga sau da dama.

Saboda ƙuncin rayuwa da dogon shiru daga ɓangaren hukumomi, ya yanke shawarar amfani da kafafen sada zumunta don riƙon a cire masa takunkumin albashinsa. Ya bayyana cewa yana da iyali da ya ke kula da su, kuma matsin tattalin arziƙi ya ƙara dagula lamarinsa.

A martaninta, hukumar kula da Malaman Jihar Borno (TSB) ta musanta zargin dakatar da albashin malamai saboda rashin halartar aiki na mako uku kacal. Jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar, Zara Aji Monguno, ta bayyana cewa kawai malamai da suka daɗe ba tare da sun halarci aiki ba, kamar tsawon zangon karatu, aka dakatar da albashinsu. Ta kuma ce sabon shugaban hukumar ya fara ɗaukar matakan mayar da albashin malamai da abin ya shafa, kuma wasu sun riga sun fara karɓar haƙƙoƙinsu. Duk da haka, ta jaddada cewa dole ne a bi ƙa’idojin neman izinin rashin zuwa aiki.

Sai dai Bukar ya musanta wannan iƙirari, yana mai cewa ya sanar da shugabansa kuma ya bi duk matakan da suka dace, amma har yanzu ba a bi masa haƙƙinsa ba. Ya ce sau da dama an buƙaci ya kawo bayanan asusun ajiyarsa na banki don duba matsalarsa, amma babu wani canji. Duk da cewa shugaban makarantar ya wanke shi daga zargin guduwa daga aiki, har yanzu ba a mayar masa da albashinsa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Nan Ba Da Jimawa Ba Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ƙirar Nijeriya Zai Fara Tashi – NASENI

Nan Ba Da Jimawa Ba Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ƙirar Nijeriya Zai Fara Tashi – NASENI

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version