LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma'ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

byShehu Yahaya
2 years ago
LEADERSHIP

Biyo bayan gagarumar gudummawar da yake bayarwa a Jaridar LEADERSHIP Hausa wajen gabatar da darussan addini a shafin Dausayin Musulunci tun daga 2014, Mahukuntan Kamfanin LEADERSHIP sun mika takardar yabo da godiya ga Shehu Isma’il Umar Almadda da aka fi sani da “Mai Diwani”, a zawiyyarsa da ke Tudun Wada, Kaduna.

Mahukunta kamfanin sun ce babu shakka Shehu Isma’il Umar Almadda, ya zama zakaran gwajin dafi wajen jajircewarsa kan kula da shafin na tsawon shekaru akalla 10, wanda hakan ya sanya suka mika masa takardar jinjina da yabo a kan namijin kokarinsa.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Babban Editan LEADERSHIP Hausa, Abdulrazak Yahuza Jere, ne ya mika takardar yabon a madadin hukumar gudanarwar kamfanin LEADERSHIP.

Mika takardar yabon, ta zo daidai da ranar bude tafsirin watan Ramadana wanda Shehu Isma’il Umar Almadda yake gabatarwa a duk shekara a Zawiyyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group da ke Tudun Wada, cikin Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

Da yake jawabi kafin mika takardar, Babban Editan, ya jaddada muhimmancin rubutun da Shehu Isma’il Umar Almadda yake yi na ilmantar da al’umma a bangaren daban-daban da suka shafi addinin Musulunci tare da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da cewa a duk Juma’a shafin Dausayin Musulunci yana fita ba tare da fashi ko sau daya ba, don haka ya ce ya ce lallai wannan abin a yaba ne.

“Ba mu taba samun marubuci da ya jima yana ba da gudunmawa a LEADERSHIP Hausa kamar Shehu Isma’ila Umar Almadda ba. Karatuttukan da yake gabatarwa sun samu karbuwa a wurin jama’a bisa irin sakonnin da ake aiko mana a kai. Tun daga kan tarihin Annabi (SAW) da matsayinsa a wurin Allah da dabi’unsa da halayensa, da hukunce-hukuncen ibada da sauran karatuttukan da yake gabatarwa a shafin masu ilmantar ga al’umma sosai da kara wanzar da zaman lafiya. A madadin mahukuntan kamfaninmu, tun daga kan Shugaba, Madam Zainab Nda-Isaiah, da mataimakinta na farko, Azu Ishiekwene, da mataimaki na biyu, Mike Okpere da Manajan Darakta, Mu’azu Elazeh da Darktan Tarurruka, Abraham Nda-Isaiah da dukkan sauran mahukunta da manya da kananan ma’aikatan Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, muna godiya.” In ji Abdulrazak.

A nashi bangaren, Shehu Isma’il Umar Almadda ya bayyana gamsuwarsa bisa karramashi da Kamfanin LEADERSHIP ya yi masa. Ya yi alkawarin ci gaba da bayar da gudummawarsa wajen ilmantar da al’umma kan lamuran da suka shafi addinin Musulunci.

Tun da farko, da yake bude tafsirin na bana, Shehu Isma’il Umar Almadda, ya dauki lokaci yana bayani kan sirrorin Alkur’ani mai girma da falalarsa da kuma addu’o’in samun zaman lafiya da kawar da kuncin rayuwa a Nijeriya da dukkan sauran kasashen duniya musamman Falasdin da Isra’ila take muzguna musu.

Malamai daga wurare daban-daban sun samu halartar bude tafsirin shehin na bana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version