CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Leadership: Za A Kara Kyautata Huldar Dake Tsakanin Najeriya Da Sin Cikin Shekaru 50 Masu Zuwa

by CRI Hausa
February 6, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Leadership: Za A Kara Kyautata Huldar Dake Tsakanin Najeriya Da Sin Cikin Shekaru 50 Masu Zuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Jaridar “Leadership” ta Najeriya ta wallafa wani bayani da Issa Aremu ya rubuta, mai taken “Kara kyautata huldar dake tsakanin Najeriya da Sin cikin shekaru 50 masu zuwa.” Cikin bayanin, Issa Aremu, ya kwatanta hanyoyin da kasashen Najeriya da Sin suka bi don neman raya kansu. A ganinsa, dalilin da ya sa ake samun bambanci sosai tsakanin kasashen 2 ta fuskar ci gaban tattalin arziki shi ne, zabin mabambantan hanyoyin raya kasa da kasashen suka yi.
Malam Issa ya kara da cewa, kasar Sin wata babbar kasa ce mai tasiri a duniya. Kuma duk wanda yake yunkurin neman ta da zaune-tsaye a kasar, sam ba zai samu nasara ba. Ya ce zuwa yanzu, kasar Sin dake bin tsarin siyasa na gurguzu ta riga ta zama kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya, kana ta samu shawo kan yaduwar cutar COVID-19 cikin nasara. Ya kara da cewa, Najeriya da Sin duk kasashe ne masu tasowa, amma hakika akwai gibi sosai tsakanin kasashen, a fannin neman ci gaba. A cewarsa, kasar Sin ta zabi turba mai dacewa a kokarinta na raya kanta, tare da nuna wa mutanen duniya irin nasarorin da kasa za ta iya samu, muddin tana da hakuri da jajircewa, da kokarin sauke nauyin dake wuyanta.
Har ila yau, Malam Issa ya kara da cewa, zuwa bana, kasashen Najeriya da Sin sun kwashe shekaru 50 suna kokarin kyautata huldar diplomasiya a tsakaninsu, lamarin da ya shaida cewa kasar Sin aminiyar Najeriya ce, wadda za a iya dogaro da ita. Ya ce ya kamata Najeriya a nata bangaren, ta zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da Sin, da koyon fasahohin kasar a fannin raya kasa. (Bello Wang)

SendShareTweetShare
Previous Post

CNN: Kwararru Sun Ce Dakin Gwajin Kwayoyin Halittu Na Wuhan Na Da Tsaro

Next Post

An Shigar Da Kayayyakin Tarihi Da Aka Gada Daga Kaka Da Kakanni Cikin Gidajen Al’umma

RelatedPosts

Muradun Raya Kasar Sin Sun Baiwa Duniya Tabbacin Bunkasuwa

Muradun Raya Kasar Sin Sun Baiwa Duniya Tabbacin Bunkasuwa

by CRI Hausa
24 mins ago
0

Daga CRI Hausa A yau Juma’a ne aka bude taron...

An Gudanar Da Taruka Biyu Na Bana A Wani Muhimmin Lokaci

An Gudanar Da Taruka Biyu Na Bana A Wani Muhimmin Lokaci

by CRI Hausa
29 mins ago
0

Daga CRI Hausa A wannan shekara ce, Jam’iyyar Kwaminis ta...

Li Keqiang: Karuwar GDPn Sin Zai Iya Zarce Kashi 6% a 2021

Li Keqiang: Karuwar GDPn Sin Zai Iya Zarce Kashi 6% a 2021

by CRI Hausa
33 mins ago
0

Daga CRI Hausa Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gabatar...

Next Post
An Shigar Da Kayayyakin Tarihi Da Aka Gada Daga Kaka Da Kakanni Cikin Gidajen Al’umma

An Shigar Da Kayayyakin Tarihi Da Aka Gada Daga Kaka Da Kakanni Cikin Gidajen Al’umma

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version