Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Likitoci 15 Sun Kamu Da Korona A Nasarawa

by Muhammad
January 12, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Likitoci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Babban Daraktan Likitoci (CMD) na asibitin kwararru ta Dalhatu Araf (DASH) da ke garin Lafia, Dakta Ikrama Hassan ya shaida cewar, daga cikin Likitocinsu 139 da suke aiki a asibitin, 15 daga ciki sun kamu da cutar Korona.

samndaads

Ya karyata ikirarin kungiyar Likitocin jihar da ke cewa Likitoci 35 ne suka kamu da cutar.

Da ya ke jawabi a karshen mako a Lafia, CMD, ya roki kungiyar likitocin da su amince da zaman tattaunawa da hukumar gudanarwa na asibitin DASH kan matsayarsu na rufe asibitin lura da barkewa annobar korona na biyu.

Ya na mai cewa, babban abun da ke akwai kan barkewar cutar a karo na biyu shine maida hankali sosai wajen ganin an bi hanyoyin dakile yaduwar cutar.

“Abun da muke cewa shine mu zauna mu yi magana kan abubuwan da suke akwai. Idan mutum uku sun kamu da cutar a wani sashi guda, hakan bai zama ya dace a rufe sauran sashi-sahi ba wanda babu wani guda da aka samu ya kamu da cutar a cikinsu.”

A cewarsa, hakki ne a kan hukumar gudanarwa na asibitin su tabbatar da kare ma’aikata ta hanyar samar musu da dukkanin kayayyakin kariya da za su basu damar gudanar da ayyukansu cikin kwanciyar hankali.

Ya ce, sun dauka kuma suna kan daukan matakan da suka dace wajen kula da lafiyar majinyata ba tare da cutar da masu aiki ko shafar ma wasu cutar da suke dauke da su ba.

Ya ce, sun bada shawarorin dukkanin matakan kariya daga cutar ake bin su.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Zulum Ya Shigar Da ’Ya’yan ’Yan Hijira 1,163 Firamari A Damasak

Next Post

Zulum Ya Tallafa Wa Manoma Da ’Yan Gudun Hijira 11,200 A Damasak

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Damasak

Zulum Ya Tallafa Wa Manoma Da ’Yan Gudun Hijira 11,200 A Damasak

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version