Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Limamin Bauchi Ya Shawarci Maniyyata Su Tsarkake Niyyarsu Tare Da Yi Wa Kasa Addu’a

by
4 years ago
in RAHOTANNI
1 min read
Limamin Bauchi Ya  Shawarci Maniyyata Su Tsarkake Niyyarsu Tare Da Yi Wa Kasa Addu’a
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Babban limamin masallacin Bauchi Alhaji Bala Ahmad Baban Inna, ya shawarci maniyyata aikin hajjin bana musamman wadanda  suka fito daga jihar Bauchi da su tsarkake niyyarsu a yayin tafiya ibadar aikin hajji don samun ayyuka karbabbu da za su sa a amshi dukkan addu’o’in da suka gudanar a yayin da suke kasa mai tsarki.

Alhaji Bala Ahmed ya bayyana hakaa ne cikin hirarsa da wakilinmu a Bauchi, inda ya kara da cewa yin wannan kira ya zamo dole domin tunatar da jama’a su lura da makudan kudin da suka kashe don tafiya sauke farali a bana. Saboda bai dace ba mutum ya kashe kudi masu yawa don yin wannan tafiya ta ibada amma ya sake wajen yin wasu ayyuka da za su haifar da nakasu game da karbar ayyukansa.

Don haka ya ja hankalin maniyyatan da su gabatar da ibada mai kyau ta hanyar tsarkake niyya da nisantar  maganganu da ke lalata ayyukan Hajji ta hanyar nisantar yin munanan maganganu ko yasasshiyar magana da sauran ayyuka munana wadanda ke bata aikin Hajjin da aka yi takakkiya don aiwatarwa da nufin samun gafarar Allah madaukakin Sarki.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

Babban limamin na Bauchin har wa yau ya roki maniyyatan da su doge wajen yi wa Nijeriya addu’ar samun inganyaccen zaman lafiya da yalwar arziki. Musamman a wannan lokacin da lamurra na zubàr da jinin bayin Allah ke kara yawaita a wasu sassa na kasar nan. Don haka  akwai bukatar maniyyata su himmatu wajen yin addu’a domin Allah ya kawo saukin abin da ke faruwa da kuma yalwar arziki a kasar nan, don jama’a su fita daga cikin kuncin rayuwa da ake fama da shi a wannan lokacin.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Bakonmu Na Mako: Na Kawo Karshen Rikicen-Rikicen Da Suka Hana Ci Gaban Jami’ar Dutsen-Ma —Farfesa Arma Ya’u

Next Post

DPP Za Ta Kawo Canjin Da Manyan Jam’iyyu Ba Su Iya Kawo Wa Ba – Juliet Ogbo

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
17 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
18 hours ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
21 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post
DPP Za Ta Kawo Canjin Da Manyan Jam’iyyu Ba Su Iya Kawo Wa Ba – Juliet Ogbo

DPP Za Ta Kawo Canjin Da Manyan Jam’iyyu Ba Su Iya Kawo Wa Ba - Juliet Ogbo

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: