Ma’aikata Sun Dukufa Domin Ceto Wadanda Girgizar Kasa Ta Aukawa A Lardin Sichuan
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikata Sun Dukufa Domin Ceto Wadanda Girgizar Kasa Ta Aukawa A Lardin Sichuan

byCMG Hausa
3 years ago
girgizar kasa

Mahukunta a lardin Sichuan na kudu maso yammacin kasar Sin, sun ce girgizar kasa mai karfin maki 6.8 da ta auku a gundumar Luding ta hallaka mutane 46. 

Mataimakin darakta a ofishin lura da ayyukan gaggawa na lardin Wang Feng ya ce, girgizar kasar ta auku ne a jiya Litinin, kuma baya ga wadanda aka tabbatar da rasuwarsu, ibtila’in ya sabbaba jikkatar sama da mutane 50, yayin da wasu 16 suka bace.

  • Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 5, Ya Lalata Gidaje 3,813 A Katsina

Mahukuntan lardin sun ce an shiga aiki gadan gadan, domin shawo kan ibtila’in, inda ya zuwa karfe 6 na yammacin jiya Litinin, masu aikin ceto sama da 6,500, da jirage masu saukar ungulu 4, da jirage marasa matuka 2 sun isa wurin domin gaggauta aikin ceton al’umma.

Masu aikin jinya daga cibiyar kula da lafiya ta Moxi, da sauran kauyuka da garuruwa makwanfa, sun gaggauta isa wurin da girgizar kasar ta auku, inda ya zuwa karfe 8 na dare, sama da wadanda suka jikkata 50 suka samu kulawar jami’an jinya dake wurin.

Kaza lika ya zuwa yanzu, rukunin ’yan sandan musamman dake aiki a wurin, sun yi nasarar ceto sama da mutum 30, da suka makale cikin baraguzan gine gine.

Bugu da kari, ma’aikatar kudi, da ma’aikatar ayyukan gaggawa, sun ware kudin Sin yuan miliyan 50, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 7.25, domin tallafawa ayyukan ceto da ba da agajin gaggawa. Ita ma gwamnatin lardin ta fitar da kudin Sin yuan miliyan 50, domin tallafawa yankin Ganzi na lardin na Sichuan.

Tuni aka samar da kayayyakin jin kai da suka hada da sama da tantuna 3,000, da gadajen tafi da gidan ka 10,000 ga gundumar Luding, inda ibtila’in ya fi kamari. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Da Dumi-dumi: Dan Lamido Da Wasu Yan Takarar Gwamna 16 Na PDP Sun Ziyarci Wike

Da Dumi-dumi: Dan Lamido Da Wasu Yan Takarar Gwamna 16 Na PDP Sun Ziyarci Wike

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version