Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Gudanar Da Liyafar Sabuwar Shekara
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Gudanar Da Liyafar Sabuwar Shekara

byCGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Sin

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya karbi bakuncin liyafar sabuwar shekara ta ma’aikatarsa, jiya Jumma’a a cibiyar gabatar da wasannin fasahohi ta Beijing.

Wang Yi ya bayyana cewa, harkokin wajen Sin sun daukaka burin gina al’umma mai makoma ta bai daya ga bil adama, da ingiza zaman lafiya da sauke nauyin da ya dace domin samun ci gaba. Ya kuma jaddada cewa, harkokin diplomasiyya na kasar Sin, sun bayar da gagarumar gudunmowa ga karin zaman lafiya da kuzari ga duniya mara tabbas.

  • An Saki Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
  • AC Milan Ta Kammala Ɗaukar Kyle Walker Daga Manchester City A Matsayin Aro

A cewarsa, kasar Sin ta shirya aiki da dukkan kasashe wajen bayar da fifiko ga zaman lafiyar duniya da shawo kan rikice-rikice da rarrabuwar kawuna da inganta abota da hadin gwiwa. Yana mai cewa “mu hada hannu tare, mu inganta fahimtar juna tsakanin mabambantan al’adu da gina al’umma mai makoma ta bai daya ga bil adama.”

A nasa bangare, jakadan Kamaru a kasar Sin, kuma shugaban kungiyar jami’an diplomasiyya dake Sin, Martin Mpana, ya yi wa al’ummar Sinawa fatan alheri a sabuwar shekara, a madadin kungiyar. Ya kuma yabawa manufar diplomasiyyar kasar Sin, bisa yadda take sauke nauyin dake wuyanta a matsayinta na babbar kasa, kuma mai bayar da gudunmowa ga warware matsalolin rashin tabbas da kalubalen duniya. Ya kara da cewa, kasa da kasa na son zurfafa abota da karfafa musaya da inganta hadin gwiwa da Sin, domin gina al’umma mai makoma ta bai daya ga bil adama.

Liyafar ta samu halartar Yin Li, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS kuma sakataren kwamitin jam’iyyar na birnin Beijing, da jami’an diplomasiyya daga kasashe daban-daban da wakilan hukumomin kasa da kasa dake Sin da jami’ai daga sassan gwamnatin kasar Sin. An yi kiyasin mutane kimanin 400 ne suka halarci liyafar. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?

Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version