Ma'aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

byAbubakar Abba
3 years ago
Kwakwa

Aikin hukumar bunkasa noman kwakwa ta Legas ce ta taimaka wajen bunkasa harkar ta yadda za a dinga samar da ita sosai ga kasuwa.

Shugaban hukumar Dapo Olakulehin ya ce jihar ita ce kan gaba wajen samar da kwakwa a kasar nan, inda ya kara da cewa, amma ba a iya wadata kasar da ita saboda karuwar masu sarrafa ta a cikin shekara 10 zuwa 15 da suka wuce.

  • Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Gudanar Da Aikin Tsabtace Muhalli A Maiduguri
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Olakulehin ya ci gaba da cewa, a shekara uku da suka wuce, lokacin da muka ga alamar karuwar bukatarta, sai muka dinga karfafa wa mutane gwiwa kan su shiga harkar domin samar da ita yadda ake bukata.

A shekara hudu zuwa biyar masu zuwa za a fara ganin tasirin hakan idan bishiyoyin suka fara ‘ya’ya, inda ya ce hukumar bunkasa noman kwakwar ta Legas tana da fili, inda take samar da dashen itaciyar da take raba wa jama’a.

Shugaban ci gaba da cewa, a bara ta raba wa manoma har dashe dubu 200 kyauta, amma duk da haka ba su isa ba, inda ya sanar da cewa, a bana kuwa dashe dubu 80 kawai hukumar ta iya raba wa, wanda wannan na nufin masu sarrafa kwakwar a Nijeriya dole ne su ci gaba da sayo ta daga waje kafin wani lokaci nan gaba.

Shi kuwa wani babban jami’i a Ma’aikatar Masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta kasa Kaura Arimiye, cewa ya yi gwamnati ta dauki wannan harka a matsayin wata hanya ta rage yawan marasa aikin yi da kuma rage dogaron da kasar ke yi a kan man fetur domin samun kudi daga kasar waje.

Wata mai kamfanin sarrafa kwakwar, wajen yin abubuwa daban-daban Ebun Feludu, ta ce, tana ganin idan gwamnati na son cim ma bukatar hakan to sai ta bunkasa muhimman abubuwan inganta rayuwa kamar wutar lantarki da tituna da sauransu.

Ta ce Nijeriya ta yi kaurin suna wajen rashin wutar lantarki, haka ma tituna ba su da kyau, inda ta kara da cewa, akwai bukatar gwamnatin ta rage hidima da kudin fitar da kayan zuwa kasuwannin duniya.

Shugabar kungiyar manoma da masu sarrafawa da sayar da kwakwar na kasa Nma Okoroji, ta ce mutane na kara samun wayewa da fahimtar cewa harka ce ta samun kudi.

Nma ta ci gaba da cewa, kwakwa za ta iya kara yawan kudin da Nijeriya ke samu, inda ta bayyana cewa, muna da kyakkyawan yanayi da filin nomanta da kuma manoman, da su yi ta.

Ta ce, muna ma fitar da ita kasashe maimakon mu sayo daga ketare, inda ta kara da cewa, mutane da yawa a Afirka ta Yamma na ci da shan ruwan kwakwa.

Ta kara da cewa , aiki karkashin wani shiri na bunkasa samar da kwakwar a kasar nan, tare da tallafin gwamnati, inda ta sanar da cewa, shirin da a karkashinsa ake kudurin dasa itatuwan kwakwa a fili mai girman hekta 10,000 a yawancin jihohin Nijeriya 36 zuwa shekara ta 2027.

Ta sanar da cewa, sai dai babbar matsalar ita ce ta samun ingantaccen irin kwakwar, inda ta ci gaba da cewa, iri ma fi inganci shi ne na aure wanda aka samar daga, hadin doguwar bishiyar kwakwar ta Afirka ta Yamma da kuma gajeruwa ta yankin Asiya.

Ta bayyana cewa, shekara hudu zuwa biyar, ba kamar gajeruwa ta Asia ba, wadda take fara ‘ya’ya a cikin shekara biyu da rabi zuwa uku, inda ta ce amma kuma ita ta aure kwararru sun samar da ita ne musamman domin noma na kasuwanci.

Shi ma wani da ke a cikin fannin mai suna Abiodun Oyelekan, ya ce yana da kyau a yi amfani da kwakwar ‘yar aure saboda yawan ‘ya’yan da take samarwa a shekara.

Ya sanar da cewa, amma tana da tsada domin duk dashe daya ya kai kusan dala shida wanda hakan ya sa ta fi karfin yawancin kananan manoman da ke a cikin fannin a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version