Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

Ma’aikatar Yada Labaran Kano Na Hada Hannu Domin Tunkarar Kalubalen Abinci Marasa Gina Jiki

by Sulaiman Ibrahim
March 4, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Ma’aikatar Yada Labaran Kano Na Hada Hannu Domin Tunkarar Kalubalen Abinci Marasa Gina Jiki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

 

Ma’aikatar yada labaran Jihar Kano za ta yi aiki tare da dukkan masu fatan taimakawa wajen magance matsalar karacin abinci mai gina jiki a Jihar Kano.

Kwamishinan Ma’aikatar yada labarai na Jihar Kano, Malam Muhammad Garba, ne ya bayyana haka a taro tattaunawar da kungiyoyin sa kai dake duba ma’aunin abinci mai gina jiki a Nijeriya (CS-SUNN) da aka gudanar a ofishinsa. Kamar yadda Jami’in yada labaran ma’aikatar Sani Abba Yola ya shaidawa LEADERSHIP A YAU.

Kwamishinan, wanda Babban Sakatare a Ma’akatar, Usman Bala Muhammad, ya wakilta yace, dabarun sadarwar da ake fatan aiwatarwa za su taimaka wajen samun nasarar yakin da ake da matsalar karancin abinci mai gina jiki.

Usman Bala ya kara da cewa matsalar karancin abinci mai gina jiki da aka yi watsi da shi sakamakon mutane sunfi mayar da hankali wajen abubuwan da ake iya gani a zahiri dake zaman kalubale ga harkokin lafiya, duk da cewa karancin abinci mai gina jiki ke haifar da mummunar illa a Kasarnan. Babban sakataren ya ci gaba da cewa matsalar a hankali na illata makomar dandazon al’ummar Jihar Kano da kasa baki daya.

Ya ce, Ma’aikatar na cikin tsarin matakan da ake kokarin aiwatarwa sannan kuma tana sane da batun abinci mai gina jiki lamari dake bukatar kulawar gaske, ya kara da cewa ya kamata a samar da wani kasafi kan wannan shiri a wannan ma’aikata.

Daga nan sai babban sakataren ya tabbatar masu da cewa ma’aikatar zata samar da jami’i guda kan lamarin karancin abinci mai gina jiki tare da yin nazarin halin da ake ciki domin samun nasarar shirin.

Tunda farko anasa jawabin, shugaban kwamitin kungiyoyin sa kan a harkar abinci mai gina jiki a kasar nan, Mr. Innocent Ekene ya bayyana cewa bayanai sun nuna cewa kashi 37% na yaran Jihar Kano na fama da irin wannan matsala wadda kuma tana da hadari kwarai ga cigaban tattalin arziki.

Shugaban ya kuma bukaci ma’aikatar yada labaran ta bujiro da wani shirin wayar da kai ta kafafen yada labarai domin fadakar da al’ummar Kano, Musamman wadanda ke zaune a karkara kan muhimmancin ingantaccen abinci mai gina jiki wanda ana iya samun sa wuraren da suke zaune.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Kafa Kwamitin Binciken Asarar Da Aka Tafka A Billiri

Next Post

Yadda Gwamnan Gombe Ya Nada Malam Danladi Maiyamba Sabon Mai Tangale

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Next Post
Sabon Mai Tangale

Yadda Gwamnan Gombe Ya Nada Malam Danladi Maiyamba Sabon Mai Tangale

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version