Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Magajin Garin Rano Da Walin Rano Sun Sha Alwashin Ciyar Da Masarautar Gaba

by
11 months ago
in LABARAI
2 min read
Rano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mustapha Ibrahim Kano

 

A ranar Juma’a da ta gabata Majalisar masarautar Rano karkashin shugabancin mai martaba sarkin Rano Alhaji kabiru Muhammad Inuwa ta nada hakimai domin taimakawa masarautar wajen cigabanta wanda suka hada da magajin garin Rano, Honarabul Adda’u Isa Rano tsohon dan majalissar wakilai mai wakiltar Rano Kibiya da Bunkure a matsayin Magajin Garin Rano, sai Alhaji Danlami Al-hassan Rano a matsayin walin rano.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Sauran su ne Dakta Yahaya Isa Bunkure, a matsayin makaman Rano a yayin da aka nada Honarabul Al-hassan Ado Doguwa amtsayin Sardaunan Rano, RT. Kabiru Al-hassan Rurum a matsayin Turakin Rano.

A jawabinsa ga manema labarai Honarabul Ada’u Isa Rano ya bayyana cewa abin da Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya yi na kir-kiro masarautar Rano da sauran masarautu biyar na Kano da kuma sahalewa mai martaba Sarkin Rano nada su a wadannan mukamai a wannan lokaci abin a yaba ne kuma ya nuna gwamnan Kano mai son cigaban al’umma ce da tarihinsu a kowanne lokaci.

Har’ila yau magajin garin Rano Honarabul Ada’u ya bayyana farin cikinsa da nada shi wannan mukami na magajin garin Rano wanda ya bayyana sarautar a matsayin sarauta mai dinbun tarihi, kuma zai yi amfani da ita wajen wayar da kan al’ummar wannan masarauta wajen a fahimci abubuwan da za su kawo cigaban zaman lafiya da karuwar tattalin arziki, tsaro da ci gaba ta kowanne fanni a wannan masarauta, inda ya bayyana mai martaba Sarkin Rano a matsayin jagoran cigaban al’umma.

Shi ma ana sa bangaren, Walin Rano ya ce wannan sarauta ta Walin Rano babbar kalubale ce a gareshi na a tashi tsaye wajen ciyar da wannan masarauta gaba, domin wannan karramawa ce daga gwamnan Kano da Mai martaba Sarkin Rano ya sa aka bashi wannan sarauta, dama sauran hakimai da aka nada a wannan rana.

ADVERTISEMENT

Alhaji Idi Gwangwan ya ce Rano ta samu jagorori da hakimai hazikai da za su ciyar da ita gaba, da Nijeriya baki daya.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Kafa Rundunar ‘Yan Sintiri Dan Magance Matsalar ‘Yan Daba Abin A Yaba Ne

Next Post

Za Mu Kara Matsin Lamba Ga Tarayya Kan Sha’anin Tsaro – Gwamna El-Rufai

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
5 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
7 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
15 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
17 hours ago
0

...

Next Post
Gwamna El-Rufai

Za Mu Kara Matsin Lamba Ga Tarayya Kan Sha’anin Tsaro – Gwamna El-Rufai

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: