Magance Matsalar Rashin Aikin Yi A Tsakanin Matasa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magance Matsalar Rashin Aikin Yi A Tsakanin Matasa

byAbdulrazaq Yahuza
2 years ago
Rashin aikin yi

Abin takaici ne a halin yanzu lamarin rashin aikin yi a tsakanin matasanmu yana ta karuwa duk kuwa da dinbin arzkin albarkatun kasa dana mutane da Allah ya hore mana.

Lamarin a duk shekara sai kara karuwa yake yi inda matasa da suka kammala karatunsu na jami’a da sauran manyan makarantu ke cika kasuwar neman aiki da fatan samarwa kansu hanyar neman rufawa kansu asiri, sai kawai su fahimci babu wata fata a garesu na samun aiki a duk inda suka fuskanta, a haka kuma zaka ga matasa da yawa suna yawo a kan titunan mu suna talla, adaidai lokacin da ya kamata a ce suna can sun samu aiki mai muhimmanci da za su fuskanci rayuwar da ta kamata. A rahoton wata cibiya mai zaman kanta mai suna JPMG yawan matasa marasa aiki a Nijeriya ya kai kashi 37.7 a shekarar 2022.

  • Zaben Gwamna: Zan Shawo Kan Matsalar Rashin Aikin Yi A Jihar Kebbi – Aminu Bande

Hasashe ya kuma nuna cewa, yawan marasa aiki zai ci gaba da karuwa zuwa kashi 40.6 a shekarar musammna ganin yadda masu neman aikin ke kara karuwa a sassan Nijeriya.

Cibiyar ta nuna tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin kasa ke yi da kuma ganin ba yadda zai iya karbar sabbin matasa fiye da miliyan 4 zuwa 5 da suke shigowa fagen fafutukar neman aiki a duk shekara. A bin talkaici a nan shi ne a halin yanzu Nijeriya ce a kan gaba a fadin duniya na kasar da ta fi kowace kasa yawan marasa aikin yi, kamar dai yadda kiddigar da aka fito da ita a kwanan nan ta nuna.

Yawan marasa aiki a Nijeriya ya kai fiye da kashi 33.3, wannan abin tsoro ne don kuwa mun zarce yawan na kasar Afirka ta Kudu da suke da kashi 32.9 da kasar Iran mai kashi 15.55. Hukumar Kididdiga ta Kasa NBS bata kai ga fitar da rahoto na wannan shekarar ba zuwa yanzu, Babu wanda zai iya karyata wannan lamarin. Rashin aiwatar da tsare-tsaren da za su kai ga bunkasa tattalin arzikin kasa ya ci gaba da zaftare abin da yake shiga aljihun al’ummar kasa gaba daya. Yadda al’ummar Nijeriya ke karuwa da kashi 3.2 yana kara tabarbare lamarin rashin aiki ga matasa. Barnar lamarin rashin aikin yi a cikin al’umma ya tashi daga na tattalin arziki zuwa haifar da kanana da manyan laifukka a tsakanin matasa a sassan Nijeriya.

Masana sun danganta karuwa rashin aikin yi a tsakanin matasa da yadda ake samun karuwar matsalar tsaro da aikata muggan aiki. Rashin aiki yana tunzura mutane fadawa ayyukan rashin gaskiya saboda neman hanyoyin neman mafita na rayuwa, wanda hakan kuma ke haifar da karywar matsalolin tsaro a sassan Nijeriya. Wani abin tayar da hankali kuma shi ne yadda matsalolin tsaro kamar fashi da makami, kashe-kashe, garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci suka ci gaba da karuwa sadoda yadda masata ke fuskantar rashin aikin yi kuma gashi suna so rafa wa kansu asiri.

Tsaface-tsaface, da yadda ake karrama wadanda suka yi kudi ta hanyar da bata dace ba, a bayyana yake a halin yanzu kungiyoyin masu aikata laifukka suna ta kara karfi a sassan Nijeriya. Jami’an tsaro na ta fafutukar ganin sun kawo karshen masu aikata laifi ba tare da samun nasarar da ake bukata ba, haka ya kai wasu gwamnoni sun yi watsi da hakkin da yake kansu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma sun bar al’umma a hannun ‘yan ta’adda suna cin karensu babu babbaka. Ayyukan ta’addanci da dama da suka hada da garkuwa da mutane da zaluntar marasa karfi yana ta daukar sabon salo a cikin al’umma. Wadannan ayyyukan ta’addanci yana kara karfafa karin maganan nan ne da ke cewa, zuciyar da ba a bata aiki ba za ta nema wa kanta aiki.”

Ra’ayin wannan jaridar a nan shi ne, wadannan matsalolin sun taimaka matuka wajen durkushe ci gaban kasar nan. Binciken da aka gudanar daban-daban musamman ma wanda Ezeajughu Mary C. (PhD), ya yi, ya nuna danganta ta kut da kut a tsakanin rashin aikin yi da yadda ayyyukan ta’addanci suke habbakar a Nijeriya.

Babu shakka a kwai hanyoyin magance matsalaer rashin aikin yi a tsakanin matasa, wanda baya ga magance matsalolin tsaro zai kuma tabbatar da bunkasar tattalin arzikin kasa ba tare da bata lokaci ba. A kan haka ya kamata dukkan gwamnatoci a dukkan mataki su karfafa kokarin su na samarwa matasa ayyukan yi a duk inda suke a fadin kasar nan.

Ganin muhimman kanana da matsaikar masanan’antu da kuma yadda manyan kamfanoni ke gudu zuwa kasashen su, ya kamata a rungumi farfado da sabbin kananan masa’anantu ta haka za a tabbatar da bunkasar tattalin arzikin kasa.

Dole gwamnati ta samar da yanayi mai muhimmanci da zai kai ga bunkasa rayuwar matasa tare da samar musu da ayyukan yi, wannan na daga cikin abubuwan da za su kawar da hankalinsu daga aikata laifukka, a kan haka a kwai bukatar samar da dokokin da za su rage wahalhalun da ake fuskanta wajen kafa kamfanoni da cire harajin da ake karba a wajen masu niyyar kafa masana’antun a fadin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa

Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version