Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Magidanci Ya Caka Wa Sakakkiyar Matarsa Wuka A Harabar Kotu

by Abdullahi Muhammad Sheka
January 29, 2021
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani magidanci ya sari tsohuwar matarsa da ke dauke da juna biyu tare

da yayanta jim kadan bayan fitowarsu daga Babbar Kotun Shari’ar
Musulunci da ke karamar hukumar Rano a Jihar Kano.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin da ta gabata, bayan da matar ta
shigar da kara kotu aka raba auren nasu da mijin nata.

Matar mai suna Shafa’atu Sale, mazauniyar garin Unguwar Kara ce a
karamar hukumar Rano, ta bayyana cewa, fitowarsu ke da wuya daga kotu
ne bayan Alkali ya raba aurensu da mijin nata mai suna Biliya
Abdullahi, sai kawai ji ta yi ya rufe ta da sara ita da yayanta mai
suna Ado Sale.

“Alkalin Kotun ya ce, na ba shi sadakinsa Naira dubu ashirin, amma sai
ya ki karba, sai Alkali ya karba a hannun Ado.

“Bayan mun fito daga kotun ne, tsohon maigidan nawa ya rika bin mu,
daga bisani kuma ya zaro wuka ya fara caka wa Ado a cikinsa, sannan ni
ma ya dawo kaina yana caka min,” a cewar matar.

Shi ma yayan nata Ado Sale ya bayyana cewa, bayan an sallame su daga
kotun ne sai ya biyo su ta baya, inda ya caka min wukar a cikina da
sauran sassan jikina.

“Da kyar na ruga da gudu zuwa bakin kotun, ban yi zaton ita ma zai
caka mata wukar ba, dga nan ne kuma sai ‘yan sanda suka zo suka cafke
shi da kyar domin kuwa har sai da suka harba bindiga,” a cewar tasa.

‘Yan sanda na cigaba da binciken lamarin wanda da zarar sun kammala za
su gabatar da shi a gaban kuliya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Matasa Su Tashi Tsaye Wajen Neman Na Kansu – Yusuf Mugamu 

Next Post

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Umurnin Kotu Na Yashe Asusun Tsohon Gwamna Yari

RelatedPosts

An Yi Wa Mukarraban Buhari Rigakafin Cutar Korona

An Yi Wa Mukarraban Buhari Rigakafin Cutar Korona

by Abdullahi Muhammad Sheka
2 hours ago
0

  Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ayau...

Farashin Gangar Danyen Man Fetur Ya Kai Dalla 71.28

Farashin Gangar Danyen Man Fetur Ya Kai Dalla 71.28

by Abdullahi Muhammad Sheka
3 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim A karon farko a 2021, farashin mai...

Naira

Naira Na Shirin Sake Faduwa Warwas – FMDQ

by Abdullahi Muhammad Sheka
10 hours ago
0

Za Ta Iya Kai Wa Dala 500 Cikin Mako Mai...

Next Post
Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Umurnin Kotu Na Yashe Asusun Tsohon Gwamna Yari

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Umurnin Kotu Na Yashe Asusun Tsohon Gwamna Yari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version