Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

byMuhammad
2 years ago
Taraba

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari garin Pupule na yankin karamar hukumar Yorro ta jihar Taraba, inda suka sace mutum 23 ciki har da basarake mai daraja ta biyu da fadawansa.

BBC ta rawaito cewa, lamarin ya afku ne a ranar Talata da daddare inda ‘yan bindigar masu yawan gaske suka shiga garin tare da kewaye shi.

  • An Sace Mai Ciki, Hakimi Da ‘Yansanda A Taraba
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Wani mazaunin garin ya shaida wa BBC cewa, ba su san adadin ‘yan bindigar da suka shiga garin nasu ba saboda yawansu.

Ya ce,” sun shiga cikin dare suka dauki na dauka suka bar na bari, kuma a cikin wadanda suka dauka baya ga basaraken da dogarinsa, akwai limamin masallacin Jumma’a da fastoci biyu da kuma sauran jama’ar gari.”

Ya ƙara da cewa ‘yan bindigar sun fasa shaguna tare da satar kayan abinci da abubuwan sha.

“Ba wannan ne zuwan su na farko ba, wannan shi ne karo na hudu da suka je garinmu” In ji mazaunin garin na Pupule.

Tuni dai rundunar ‘yan sanda Nijeriya reshen jihar ta Taraba ta ce ta fara bincike tare da neman mutanen da aka sacen.

Mai magana da yawun rundunar SP Abdullahi Usman Jada, ya ce suna samun labarin abin da ya farun, nan da nan kwamishinan ‘yan sandan jihar bai yi kasa a gwiwa ba ya tura wani sashe na musamman na jami’ansu wadanda ke kula da masu satar mutane domin su je garin da kuma bin sawun ‘yan bindigar.

Ya ce an baza jami’an tsaro a jejin domin neman mutanen da aka sace, “amma har yanzu ba mu ji komai ba,” a cewarsa.

Jama’ar garin na Pupule dai, sun ce a duk hare-haren da aka kai masu sau uku a can baya, wannan shi ne mafi muni da tayar da hankali, kuma sun yi kira da a girke masu karin jami’an tsaro a yankin.

Matsalar tsaro a Najeriya dai na ci gaba da zama ruwan dare gama duniya musamman ta masu satar mutane domin kudin fansa a yankunan arewa maso yammacin kasar da kuma wasu yankuna na arewa maso gabashin kasar.

Kuma duk da kokarin da gwamnatin tarayyar kasar ta ce tana yi don kawo karshen wannan matsala har yanzu ba ta sauya zani ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin $2m A Wajena, Ina Da Hujja –Matawalle

Gwamnati Ta Shirya Fatattakar 'Yan Bindiga A Duk Inda Suke - Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version