Bala kukkuru legas">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Mahauta Na Cigaba Da Samun Nasara A Legas – Sarkin Fawa

by Bala kukkuru legas
December 17, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Sarkin Fawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Sarkin Fawan Kasuwar Mile 12 Intanashinal Market a cikin garin Legas, Alhaji Usman Illela ta karamar hukumar Illela da ke cikin Jihar Sakkwato, ya bayyana cewa, shi da sauran mahauta na unguwar Mile 12 da Jihar Legas bakidaya su na cigaba da samun nasarori a wajen gudanar da harkokin sana’ar fawa a Legas da kewayanta.

Sarkin Fawan na unguwar Mile 12 ya yi wannan tsokaci ne a ofis dinsa da ke unguwar Mile 12 jim kadan bayan tashi daga taron su na mahauta da su ka saba yi a duk karshen wata, domin tattaunwa a bisa kan yadda za su kara nemo hanyoyin da za su cigaba da kawo cigaban sana’ar fawa tare da zuwan akasin hakan.

samndaads

Ya cigaba da cewa, babu shakka daga ’yan shekarun baya kadan da su ka wuce zuwa yanzu sana’ar fawa ta kara samun daukaka, idan a ka yi la’akari da irin yawan mutanen da su ka samu rufin asiri a cikinta.

A cewarsa, “wadansu sun gina gidaje, wadansu sun sayi motoci da sauran makamantansu. Da fatan Allah ubangiji ya cigaba da zaunar da Nijeriya lafiya.”

Sarkin Fawan ya cigaba da tsokaci a bisa ga irin cigaba da ya ke ganin kasuwar ta na Mile I2 ta ke kara samu a halin yanzu, ya na mai cewa, babu shakka kasuwar a halin yanzu ta na kara samun cigaba, domin kuwa ta samu shugaba tsayayye, wanda shuwagabannin bangarorin kasuwar su ke goya ma sa baya a wajen gudanar da ayyukan cigaban kasuwar.

Ya cigaba da cewa, “a halin yanzu idan ka shiga kasuwar za ka ce ka shiga kasuwar Amerika ko London ko kasuwar wata kasa makamanciyar irin wadannan kasashen da su ka cigaba, kuma shugaban kasuwar ta Mile I2 ya hada kawunan ’yan kasuwar gabadaya da sauran kabilu mazauna yankin bakidaya. Shi ya sanya al’ummar Hausawa da sauran kabilu mazauna kasuwar su ke ta sanya ma sa albarka a game da wannan al’amari.

Daga karshe ya ce, ya na mai isar da sakon ta’aziyyarsa ga iyalai da ’yan uwa da abokan arziki da kamfanin Jaridar LEADERSHIP bisa ga rasuwar shugaban kamfanin, Sam Nda-Isaiah, tare da fatan Allah ubangiji ya ba su juriyar wannan rashi da Nijeriya ta yi bakidaya.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Hada Hannu Da Kungiyar Kurame Domin Inganta Cigabansu – Mashawarciyar Ganduje

Next Post

2023: Tsoffin Sanatoci Da ’Yan Majalisa Sun Bukaci Tinubu Ya Tsaya Takara

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Bala kukkuru legas
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Bala kukkuru legas
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Bala kukkuru legas
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post
Tinubu

2023: Tsoffin Sanatoci Da ’Yan Majalisa Sun Bukaci Tinubu Ya Tsaya Takara

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version