Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home JAKAR MAGORI

Mai Gadi Ya Gayyato Barayi Don Yi Wa Mai Gidansa Fashi

by Muhammad
April 1, 2021
in JAKAR MAGORI
1 min read
Abinci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

Rundunar ‘yan sanda reshen Jihar Ondo ta cafke wani mai gadi da ke aiki a gidan mai na S.A. da ke garin Ondo, Abiodun Osuntimehin, bisa zarginsa da hannu da yi wa ofishin fashi.

Bayanai sun nuna Abiodun shi ne ya shirya fashin da aka yi a gidan man. An ce an kashe wani gadi yayin aiwatar da fashin, inda daga baya kuma suka sace Naira miliyan biyu.

Da yake gabatar da wanda ake zargin, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Mista Bolaji Salami, ya ce wanda ake zargin ya amsa laifinsa kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da shi gaban kotu.

Ya ce, “An kashe wani mai gadi kuma an sace kimanin Naira miliyan biyu daga wurin ajiyar, amma abin farin ciki shi ne mutumin da ya aikata wannan mummunan aikin nan da nan masu bincikenmu suka kama shi, wanda bai bai tabuka komai ba yayin da ake kokarin kama shi.

“Abiodun Osuntimehin, mai gadi tare da wannan kamfani, shi ne ya jagoranci aikata hakan; ya amince da aikata laifin kuma nan ba da dadewa ba za a gurfanar da shi gaban alkali domin yanke masa hukunci daidai da laifin da ya aikata,” inji shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Amfanin Gashi A Jikin Dan Adam (2)

Next Post

Matashi Ya Daba Wa Wani Wuka Har Lahira A Walimar Aure

RelatedPosts

Wiwi

NDLEA Ta Cafke Masu Fataucin Mutane Da Kwayoyi Na Naira Miliyan 564 A Abuja

by Muhammad
1 week ago
0

Babafemi ya ce wanda ake zargin mai shekaru 40 da...

kama

Yadda Danuwana Ya Tilasta Min Aikata Miyagun Laifuka –Wanda Ake Zargi

by Muhammad
1 week ago
0

A ranar Litinin Rundunar yan sandan karkashin jagorancin DCP Abbaa...

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

An Haifi Wani Yaro Da Azzakari Uku A Irak

by Muhammad
1 week ago
0

Likitoci a Iraki sun bayar da rahoton haihuwar wani jariri...

Next Post
Wuka

Matashi Ya Daba Wa Wani Wuka Har Lahira A Walimar Aure

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version