Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Mai Yiwuwa Gwamnatin Tarayya Ta Sake Dawo Da Tallafin Mai

by Muhammad
January 12, 2021
in TATTALIN ARZIKI
3 min read
Tallafin Mai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani rahoto ya bayyana cewa, sakamakon karuwar farashin mai a kasuwan duniya wanda a yanzun  haka  gwamnatin tarayyar Nijeriya na kayyade farashin mai ne biya yadda kasuwa ta ka, hakan zai iya yuwuwa  a kara dawa da tallafin  mai a Nijeriya. Tun daga ranar 13 ga watan Nuwambar shekarar 2020, farashin mai bai sake karuwa ba a cikin kasar nan, a yanzu farashin danyan mai a kasuwan duniya ya tashi daga dala 41.51 zuwa dala 51,22 ga kowacce gangan mai tun daga ranar 31 ga watan Disamba. ‘Yan kasuwan mai sun yi tsammanin samun sabon farashin mai ganin yadda danyan man yake bunkasa a kasuwan duniya. Gwamnatin tarayya ta rage naira biyar daga cikin farashin mai a ranar 14 ga watan Disamba, sakamakon gyara da aka yi a bangaren man fetur.

Karamin ministan mai Timipre Sylba ya bayyana cewa, tun daga watan Satumba na shekarar da ta gabata, gwamnatin tarayya ta dakatar da kayyade farashin mai a Nuijeriya. Ya kara da cewa, ana saka farashin ne bisa yadda kasuwa ta kayyade.

samndaads

Gwamnatin tarayya ta cire tallafin mai ne dun a watan Maris ta shekarar 2020, bayan rage farashin mai daga naira 145 zuwa naira 125 ga kowani lita daya na  man fetur. An dai ci gaba da rage farashin man har zuwa watan Yuni. ‘Yan Nijeriya sun ci gaba da fuskantar karin kudin mai na tsawan wata hudu, inda ya fara tashi tun daga naira 121.50 zuwa naira 123.50 a watan Yuni, sannan ya tashi daga naira 140.80 zuwa naira 143.80 a watan Yuli, haka kuma ya tashi daga naira 148 zuwa naira 150 a watan Agustan, a watan Satumba ya tashi daga naira 158 zuwa 162, daga karshe ya tashi daga naira 163 zuwa 170 a watan Nuwambar shekarar 2020.

A  kasuwan mai na duniya kuwa,  danyan  mai ya karu zuwa kashi 35 tun daga ranar 13 ga watan Nuwamba. Inda a ranar Juma’a kowacce gangar mai ta kai dala 55.99 wanda ya karu  na tsawan wata 11.

“Har yanzu akwai sauran burbushin tallafin mai, amma gwamnati ta karkashin kamfanin mai  suna rufe lamarin,” kamar yadda shugaban ‘yan kasuwan mai na Nijeiya, Mista Mike Osatuyi ba bayyana wa manema labarai lokacin da ya zanta da su.

Ya bayyana cewa, a cikin watan Disamba farashin man ya kusa kai 180 ga kowacce lita daya. Ya kara da cewa, da wannan farashin danyan mai a yanzu, akwai tallafin mai wanda ya kai na naira miliyan 800 ga kowacce rana a cikin litar mai guda miliyan 40 wanda masu amfani da man suke saya. Ya ci gaba da cewa, saboda ‘yan siyasa suke cinye kudaden ne ya sa ba a so a kawowa ‘yan Nijeriya sauki wanda wannan lokacin ne ‘yan Nijeriya ke matukar shan wahala a bangaren mai.

Osatuyi ya ce, “amma ya kamata gwamnatin tarayya ta bayyana wa majalisar kasa tallafin da ake bayarwa a halin yanzu. Ya kamata a fada wa ‘yan Nijeriya za a koma lokacin bayar da tallafi. Saboda bashin da gwamnatin tarayya ta amso a wajen hukumar bayar da lamuni ta duniya da kuma Bankin Duniya akwai sharadin gyara bangaren mai, ina fatan gwamnatin tarayya za ta yi kokarin dakile  matsalolin da ake fuskanta a yanzu.

“Idan an gyara bangaren mai yadda ya kamata, duk wadannan matsaloli ba za su dunga faruwa ba, amma akwai abubuwan da ke boyewa wajen gyara fannin mai a halin yanzu.” In ji shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Cikin Awa 24 Kacal, Dangote Ya Tafka Asarar Dala Miliyan 900

Next Post

Rashin Tsaro: Shugaba Buhari, Monguno Da Aikin Tattara Bayanan Sirri

RelatedPosts

Kangin Talauci

Shirin Tsamo Mutane Miliyan Biyu Daga Kangin Talauci Ya Kankama – Osinbajo

by Muhammad
2 days ago
0

Bayan samun nasarar kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki...

Talakawan Nijeriya

Talakawan Nijeriya Miliyan 24.3 Sun Samu Tallafin Naira 5,000 Kowanne – Ministar Jinkai

by Muhammad
2 days ago
0

A ranar Talata ne, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, sama...

FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) ta bayyana cewa, ta...

Next Post
Bayanan Sirri

Rashin Tsaro: Shugaba Buhari, Monguno Da Aikin Tattara Bayanan Sirri

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version