Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Binciki Shugabannin Nijeriya Kan Batun Wutar Lantarki

by
3 years ago
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Majalisar wakilan Nijeriya ta cimma matsayar gudanar da bincike dangane da makudan kudaden da gwamnatin tarayya ta biya kwangilolin magance matsalar rashin tsayayyar wutar hasken lantarki a kasar. Daya daga cikin ‘yan majalisar wakilan Honorabul Sada Soli Jibiya ne ya gabatar da kudurin a wannan Alhamis, da ya samu amincewar daukacin takwarorinsa.

Majalisar ta ce za a binciki tsohuwar gwamnatin ta Olusegun Obasanjo wacce ya jagoranta daga 1999 zuwa 2007, domin bada bahasi kan dala biliyan 16 da gwamnatin ta yi ikirarin kashewa kan inganta wutar lantarkin.

Binciken majalisar wakilan zai kuma fadada bin kwakkwafin zuwa kan gwamnatocin Marigayi Umar Musa ‘Yar Adua, Goodluck Jonathan da kuma gwamnatin mai ci karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari.

Labarai Masu Nasaba

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

A shekarar 2008 majalisar wakilan Nijeriya ta taba kaddamar da bincike kan dala biliyan 16 da tsohon shugaban kasar Obasanjo wanda ya yi ikirarin kashewa don inganta lantarki ba tare da ikirarin ya tabbata ba.

ADVERTISEMENT

A wancan lokacin, tsohuwar gwamnatin ta ce zuba makudan kudaden a fannin lantarkin zai samarwa da Nijeriya karfin wutar da zai kai Megawatts dubu 40 a shekarar 2020.

Har yanzu dai samar da hasken lantarki batu ne da ‘yan siyasar Nijeriya ke amfani da shi wajen neman kuri’a yayin yakin neman zabe, duk da ikirarin gwamnatocin da suka gabata, na zuba makudan kudade a fannin, ba tare da an ga sahihin sakamako ba.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Kasashen Afrika Na Fama Da Fari- Kungiyar Agaji Ta Oxfam

Next Post

Harin Boko Haram Ya Kashe Mutum Biyu A Borno

Labarai Masu Nasaba

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

by Abubakar Abba
8 hours ago
0

...

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

by Abubakar Abba
8 hours ago
0

...

CAN Ta Shirya Zanga-Zangar Yin Allah Wadai Da Kisan Deborah A Duk Jihohin Nijeriya

Batanci: CAN Ta Janye Gabatar Da Zanga-Zangar Da Ta Shirya Kan Kisan Deborah

by Leadership Hausa
12 hours ago
0

...

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

by Abubakar Abba
13 hours ago
0

...

Next Post
Gaidam

Harin Boko Haram Ya Kashe Mutum Biyu A Borno

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: