Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Majalisa Za Ta Tantance Sabbin Shugabannin Tsaro A Wannan Makon

by Khalid Idris Doya
February 15, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Sanatoci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban kwamitin kula da harkokin Sojoji na majalisar Dattawa, Sanata Ali Ndume ya shaida cewar hadakar Kwamitocin Majalisar na Soja, sojan sama da ta ruwa da yiyuwar su fara tantance zababbun sabbin shugabannin hukumomin tsaro a wannan makon da muke ciki.

Sanata Ndume ya bayyana hakan ne lokacin da ke amsa tambayoyi daga jaridar The Nation a Abuja.
Idan za ku iya tunawa dai a ranar Laraba ne shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan ya tura bukatar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiko na neman Majalisar ta amince da sabbin zababbun shugabannin hukumomin tsaro zuwa gaban kwamitocin majalisar kan soji, sojin sama da ta ruwa domin gudanar da aikin da ya dace a kai.
Lawan ya baiwa kwamitocin mako biyu da su kammala gudanar da ayyukan da aka ba su tare da gabatar da rahoton aikin nasu a gaban majalisar.
LEADERSHIP A YAU ta nakalto cewa sabbin zababbun shugabannin hukumomin tsaron da Buhari ya zaba sun kunshi: Manjo Janar Lucky Eluonye Onyenuchea lrabor a matsayin (shugaban ma’aikatar  tsaro); Manjo Janar Ibrahim Attahiru a matsayin (Shugaban sojojin Nijeriya); Rear Admiral Awwal Zubairu Gambo, (Shugaban sojin ruwa); da kuma Air bice Marshal Isiaka O. Amao a matsayin shugaban sojin sama.
Sun canji tsohon Shugaban ma’aikatar tsaro Janarar Abayomi Olonisakin; tsohon Shugaban Sojoji Lt-Gen. Tukur Buratai; tsohon Shugaban sojin ruwa bice Admiral Ibok Ete Ibas da kuma tsohon Shugaban sojin sama Air Marshal Sadikue Abubakar.
Da ya ke amsa tambayoyin Sanata Ndume ya lura kan cewa ba a bayyanar jama’a za su tantance Shugabannin hukumomin tsaron ba.
Ya kuma ce za dai su fara aikin tantancewar a wannan makon tun da an baiwa kwamitocin nasu mako biyu ne kawai da su gabatar da rahoton aikinsu.
Ya yi alkawarin cewa za su ke sanar da jama’a halin da ake ciki dangane da wannan aikin da aka daura musu.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Batun Matsalolin Rashin Tsaro Ya Mamaye Taron Kungiyar Fitiyanul Islam Na Kasa – Sheikh Ganganfa

Next Post

Shugaban Jaridun Manhaja Da Blueprint Ya Sabunta Rajistarsa Ta APC

RelatedPosts

Dakarun Tsaro Sun Dakatar Da Aiki A Yankin Orlu Na Jihar Imo

by Khalid Idris Doya
15 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A wani labarin kuma, Dakarun sun...

EFCC

EFCC Ta Cafke Mutum Tara Da Zargin Kutse A Yanar Gizo

by Khalid Idris Doya
15 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Jami'an hukumar yaki da cin hanci...

Soja

’Yan Sanda Sun Cafke Korarren Soja Yana Fashi

by Khalid Idris Doya
15 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wani matashi dan shekaru 27 da...

Next Post
Shugaban Jaridun Manhaja Da Blueprint Ya Sabunta Rajistarsa Ta APC

Shugaban Jaridun Manhaja Da Blueprint Ya Sabunta Rajistarsa Ta APC

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version