Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kasafin 2021 Na Tiriliyan N13.582

by Khalid Idris Doya
December 22, 2020
in LABARAI
2 min read
Majalisar Dattawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince da harsashen kasafin kudi na 2021 wanda yawansa ya kai naira Tiriliyan N13,588,027,886,175tn.

An samu karin sama da naira biliyan 500 daga kasafin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aiko na tiriliyan N13.082,420,568,233tr tun da farko. Hakan kuma ya bada damar cike gibin wasu wuraren da hadakar kwamitocin majalisar wakilai da ta dattawa suka nemi shugaban kasa da ya yi domin tabbatar da gudanar da ayyukan da za su kai ga inganta rayuwar ‘yan kasa da ciyar da kasar gaba.

samndaads

Amincewa da kasafin ya biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan kasafi ya gabatar na bada shawara kan hakan.

Shugaban kwamitin kasafi na majalisar, Sanata Jibrin Barau, ya mika rahoton nasu a gaban majalisar yayin zamanta na jiya Litinin.

Sannan kuma majalisar ta amince da tiriliyan N4,125,149,354,222 a matsayin kudin gudunmawar da za ta tattara domin gudanar da manyan ayyukan raya kasa.

Da yake nuna farin cikinsa kan amincewa da kasafin da majalisar ta yi, shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana cewar a kowani lokaci a shirye suke suke amincewa da kasafin kudi a kan lokaci domin baiwa majalisar zartarwa damar gudanar da ayyukan raya kasa.

Ya kuma ce, ya ji dadin da aka kammala gabatar da kasafin kafin bukukuwan kirisimeti da na sabuwar shekara.

“Bari na fara yi mana murnar yin aiki tukuru wurin ganin mun amince da kasafin 2021 a kan lokaci kafin tafiya hutun Kirsimeti. A shirye muke kowace shekara mu ci gaba da yin ayyukanmu a kan lokaci domin amincewa da kasafin kudi a kan kari domin bada damar gudanar da ayyukan da aka tsara na raya kasa,” a cewar shi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kotu Ta Umarci Maina Da Ya Fara Gabatar Da Shaidun Kariya A Karshen Janairu

Next Post

Maidakin Gwamnan Kano Ta Ja Hankalin Mata Kan Kula Da Awon Ciki

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Khalid Idris Doya
12 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Khalid Idris Doya
13 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Khalid Idris Doya
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post
Maidakin Gwamnan Kano

Maidakin Gwamnan Kano Ta Ja Hankalin Mata Kan Kula Da Awon Ciki

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version