Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai

byYusuf Shuaibu
1 year ago
Binciken

A yayin da jama’a ke nuna bacin rai da rashin gamsuwa sakamakon karin farashin man fetur da kuma karancinsa a kasuwanni, majalisar dattawa ta dakatar da binciken lamarin wanda ya haifar da rudani.

Jagoran majalisar dattawa kuma shugaban kwamitin binciken badakala a bangaren masana’antar man fetur ta Nijeriya, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a farkon makon nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

A cikin sanarwar da Bamidele ya fitar bai yi bayanin dalilin dage binciken ba, amma ya yi ikirarin cewa an dauki matakin ne domin amfanar da kasar nan da kuma al’ummarta.

Ya kuma bayyana cewa dage binciken ya zama wajibi bisa la’akari da bukatar da ake da ita na kara tuntubar masu ruwa da tsaki a ciki da wajen harkar man fetur da kuma majalisun dokoki domin kara zurfafa bincike a kan lamarin.

Ya ce, “Abubuwan da ke faruwa a kasar nan da suka bukatar dukkanin masu ruwa da tsaki a harkokin gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya su dauki matakin gaggawa.

“Yayin da muke matukar yin nadama kan duk wata matsala da ta shafi al’ummar kasar nan, an yanke wannan shawarar ne saboda amfanin kasa.”

Ya bayyana cewa an dauki kowanne daga cikin wadannan hukunce-hukuncen ne domin bai wa kwamitin wucin gadi damar gudanar da harkokin jin ra’ayoyin jama’a tare da samar da mafita mai dorewa kan kalubalen da ke fuskantar bangaren man fetur na kasar nan.

Majalisar dattawar ta kuma bai wa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa za a sanar da su sabuwar ranar jin ra’ayoyin jama’a nan gaba kadan.

Bincike ya nuna cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya kafa kwamitin wucin gadi da zai binciki biliyoyin da aka kashe wajen kula da matatun man kasar nan tare da binciko hukumomi da ke kula da kudaden da ake biya ga masu safara da kuma bankado zargin shigo da gurbatattun albarkatun man fetur da dizal mara inganci cikin kasar nan.

Wani bincike da aka yi ya nuna cewa kwamitin wucin gadi ya kammala gudanar da ayyukansa na bincike kafin ya gudanar da taron tattaunawa da shugabannin ma’aikatu da hukumomin da kuma wasu masu zaman kansu a bangaren man fetur na kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version