Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Majalisar Dattawa Za Ta Amince Da Kasafin 2021 Ranar Litinin

by Khalid Idris Doya
December 17, 2020
in LABARAI
1 min read
Kasafin 2021
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Sanata Ahmad Lawan, ya shaida cewar majalisar ta kimtsa domin gudanar da zama na musamman kan kasafin 2021 tare da amincewa shi a ranar Litinin mai zuwa.

Lawan ya shaida hakan ne a yayin zaman majalisar a jiya biyo bayan kudurin da Sanata Yahaya Abdullahi (APC daga mazabar Kebbi ta arewa) ya gabatar, da ya samu marawar bayan shugaban marasa rinjaye Enyinnaya Abaribe (PDP daga mazabar Abia ta kudu).

samndaads

A cewar shugaban majalisar, jinkirin amincewa da kasafin ma da aka samu tun da fari, ya biyo bayan bukatar da kwamitin majalisar kan kasafi ya yi wa gwamnati na kara yawan kudade.

“Kwamitinmu kan kasafi ya dukufa gudanar da aiki babu dare ba rana. Mun tsara amsar rahoto daga kwamitinmu kan kasafi a yau (jiya kenan) amma a sakamakon jinkirin bukatar karin kudi daga suka yi daga wajen gwamnati, muna son ne kwamitinmu ya tabbatar ya yi aiki da ababen da suka dace da kamata.

“Wannan yana sake bayyana irin yadda majalisar take da zimmar amincewa da kasafi a kan lokaci, mun yin hakan a shekarar da ta gabata, da yardar Allah za mu cigaba da yin hakan,” inji Lawan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dalilinmu Na Tallafa Wa Masu Sana’ar Kifi A Legas – Daraktan BATNF

Next Post

Yadda Mauludin ‘Yan Shi’a Ya Gudana A Legas

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Khalid Idris Doya
10 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post
Mauludin 'Yan Shi'a

Yadda Mauludin 'Yan Shi'a Ya Gudana A Legas

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version