Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Majalisar Mahaddata Ta Kasa Ta Yi Addu’ar Sabuwar Shekarar Musulunci

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka

Ranar Juma’ar da ta gabata ne al’ummar Musulmi a fadin duniya suka gudanar da tarukan addu’o’i domin shigowar sabuwar shekarar Musulunci ta 1439 bayan Hijira, Shugaban Majalisar Mahaddata Alkur’ani na kasa Sheikh Hassan Musa Minna shi ma ya jagoranci gagarumin taron addu’a da kuma saukar Alkur’ani da majalisar ta shirya a fadin kasarnan domin neman Allah Ya kara kawowa Nijeriya zaman lafiya, kwanciyar hankali da yalwar arziki.

Sheikh Hassan Musa Minna ya ce mai alfarma Sarkin Musulmi Dakta Sa’ad Abubakar III ya bayyana ranar Juma’a a matsayin ranar daya ga watan Almuharram, saboda haka Majalisar Mahaddata ta dauki wanann rana ta zama ranar haduwa da ‘yan uwa mahaddata Alkur’ani domin gudanar da addu’o’i tare da jaddada rokon Allah ya karawa shugaban kasa lafiya, haka kuma Majalisar ta hori daukacin Mahaddata Alkur’ani da su shigar da kasa cikin addu’o’i a duk lokutan karatukansu.

Da yake karin haske kan kokarin mai Alfarma Sarkin Musulmi na inganta harkar tsangayu da karatun Alkur’ani, shugaban ya bayyana aniyar alarammomi na ganin sun karbi dukkan wani gyara da kuma shawarwarin da za’a gabatar a lokacin taron da za’a gudanar a Kaduna cikin makon nan, saboda haka Gwani Hassan Musa Minna ya tabbatarwa ‘yan uwa kyakkyawar aniyar shugaban kasa na ciyar da harkar ilimi gaba. shugaban mahaddatan ya bukaci gwamnatoci a matakin kasa da jihohi da su ci gaba da tuntubar masu ruwa da tsaki akan harkar tsangayu a duk lokacin da ake shirin kawo wani gyara a harkar tsangayunmu, muna tabbatarwa hukumomin samun hadin kan mu a ko da yaushe” in ji shi.

Shugabann ya yi doguwar nasiha ga jama’a da cewar shigowar sabuwar shekarar Musulunci ba lokaci ne na bushaha ko holewa ba ne, kamata ya yi jama’a su waiwaya baya su ga menene ya faru a shekarar da ta gabata, inda ake bukatar gyara sai a kudiri aniyar gyarawa a cikin wanann sabuwar shekara, kuma dole jama’a su rungumi zaman lafiya da abokan zamansu, domin addinin musulunci ya nuna mana alfanun kyautata zamantakewa. Saboda haka shugaban ya yi addu’ar Allah ya kara mana zaman lafiya a kasarmu baki daya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sheikh Dahiru Ya Shirya Addu’ar Sabuwar Shekarar Musulunci

Next Post

Shugaban Rundunar ’Yan Sanda Ya Gargadi Jami’ansa Kan Cin Hanci

RelatedPosts

Lantarki

Gwamantin Tarayya Ta Yi Bayani Game Matsalar Karancin Wutar Lantarki A Kasar

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Ministan Wutar lantarki, Injiniya Sale Mamman,...

Direbobi

Satar Mutane A Manyan Hanyoyi: Direbobi A Zamfara Sun Tsunduma Yajin Aiki

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Direbobin abeben hawa na haya masu...

Gwamnonin

Gwamnonin Nijeriya Sun Koka Kan Tabarbarewar Tsaro

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Kungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta nuna...

Next Post

Shugaban Rundunar ’Yan Sanda Ya Gargadi Jami’ansa Kan Cin Hanci

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version