Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Majalisar Neja Za Ta Samar Da Dokar Hukunta Masu Bai Wa ’Yan Bindiga Bayanai

by Muhammad
February 22, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Majalisar Neja
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar,

Majalisar dokokin Neja ta bayyana kudurinta na samar da dokar da ta shafi garkuwa da jama’a na hukunta mutanen da ke tsegunta wa ‘yan bindiga bayanan jama’a a jihar.

samndaads

Shugaban majalisar dokokin, Rt. Hon. Abdullahi Bawa Wuse ne ya bayyana hakan a lokacin da ya jagoranci majalisar fadar gwamnatin jihar dan jajantawa gwamna kan harin daliban makaranta tare fasijojin NSTA da ake garkuwa da su a halin yanzu.

“Mun tsayar da wannan satin, za mu gyara akan dokar da ta shafi garkuwa da jama’a da mu sanya masu baiwa ‘tan bindiga bayanai dan hukunta su.”

Majalisar ta shawarci gwamnatin da ta shirya taruka da sarakuna kuma ta ba su damar sanya ido akan kula da shigar baki a yankunan su, shugaban majalisar yace majalisar dokokin jihar a shirye ta ke dan taimakawa da duk hanyar da ta dace wajen kawo karshen rashin tsaro a jihar.

Shugaban majalisar ya yi tir da wannan nummunar barnar da ya faru a Kagara da kuma wasu kauyukan, ya kara da cewar akwai bukatar kowa ga Allah dan sanun nafita.

A bayaninsa, gwamna Abubakar Sani Bello ya yabawa majalisar akan irin nuna goyon bayanta ga jihar kuma yayi na’am da waiwayo dokar da ta shafi garkuwa da jama’a dan hukunta masu tseguntawa ‘yan bindiga bayanan jama’a.

Ya nuna damuwarsa akan hare-haren da ‘yan bindigar ke kaiwa wasu sassan jihar nan, kuma ya bada tabbacin zai dauki matakan da suka dace dan dawo da dalibai da fasinjojin da ake garkuwa da su ga iyalansu.

” Muna cigaba da daukar matakan sanya ido dan sanin asalin inda aka samo tushen matsalolin rashin tsaron da muke fuskanta, da irin matakan da ya dace mu dauka”.

Gwamna ya bayyana cewar akwai taruka da dama da muka yi da sarakuna, wanda muna ba su damar bin matakan da suka dace wajen sanya ido akan yadda ake gudanar harkokin yau da kullun a yankunan su kuma su rika sanar da hukumomin da suka dace, kuma za mu cigaba da shirya tarukan da su.

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sanda Sun Cafke Barayin Mutane Da Kwato Bindigogin Biyu

Next Post

Jinkirin Bai Wa Manoma Kayan Aiki Na Janyo Wa Noma Illa – Makarfi

RelatedPosts

Ummu-Kalthum Sambo

Tallan ’Ya’ya Mata Kalubale Ne Babba – Ummu-Kalthum Sambo

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Daga Idris Umar,Zariya   A cikin makon daya gabacemu ne...

Ihiya'ussuna

Makarantar Ihiya’ussuna Ta Yi Sauka Karo Na Tara

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Daga Idris Umar Zariya   Madarasatu ihiya'ussuna school of Arabic...

NARICT

NARICT: ’Yan Kungiyoyi Sun Yaba Wa Cigaban Da Farfesa Barminas Ke Samarwa A Zariya

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Daga Idris Umar, Zariya   Mambobin kungiyoyin al'umma da ke...

Next Post
Makarfi

Jinkirin Bai Wa Manoma Kayan Aiki Na Janyo Wa Noma Illa – Makarfi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version