Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Majalisun Dokokin Jihohi Sun Kafa Kwamiti Don Duba Yiwuwar Gyara Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
March 29, 2021
in LABARAI
2 min read
Majalisun Dokokin Jihohi Sun Kafa Kwamiti Don Duba Yiwuwar Gyara Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

 

Shugabannin (Kakaki) Majalisun Dokokin Jihohin Kasar nan sun kare taron su na tuntubar juna a garin Bauchi, inda suka kafa kwamiti da za duba yiwuwar wanzar da canje-canje a cikin kundin tsarin   mulkin kasar nan domin yin kwaskwarima ga wasu batutuwan da suke ganin kasar za ta ci gaba idan aka waiwayesu.

Taron na Kakakin Majalisun Dokoki na jihohi 36 na kasar nan ya bayyana cewar, an baiwa kwamitin hurumin yin nazari kan bukatun canje-canje na majalisun, da kuma gabatar da tsarin nasu majalisun ga kwaryar sake duba tsarin mulki kasa dake gudana a halin yanzu.

Shugaban Zaure Majalisun Dokokin Jihohin wanda kuma shi ne Kakakin Majalisar Jihar Bauchi, Rt. Hon. Abubakar Yakubu Sulaiman shine ya bayyana kudirorin taron wanda ya duba lamura masu yawa da suka jibanci kasar nan.

Gaba-gaba cikin lamuran shine na matsalar rashin tsaro da ta addabi kasar nan, a inda taron ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta mayar da hankali kan wannan lamari domin ya tafi bai daya da taswirar tsirurukan kasar nan

Rt. Hon. Abubakar Suleiman ya bayyana cewar, taron wanda aka gudanar a Otal da Makwatan Hazibal dake cikin garin Bauchi ya karkata bakin sa ne wajen baiwa kasar nan tsaro ta hanyar hadin kai wanda ya kunshi hukumomin tsaro da al’ummomin kasa doin shawo kan lamarin.

Jawabin bayan taro taron ya kuma bukaci daukacin Majalisun Dokoki na jihohin kasar nan da su amince da dokar kasafta kudaden rabo na kasar nan yadda zai wanzar wa majalisun dokoki da fannonin shari’a cin gashin kansu.

Taron, wanda Kakaki na Majalisun Dokokin jihohi 36 da mataimakan su daga wasu jihohi suka halarta ya kuma nemi kungiyar ma’aikatan majalisun dokoki na jihohin kasar nan (PASAN) da su mayar da wukaken su zuwa kube dangane da koke-koken, ko bukace-bukacen da suke da su.

Kamar yadda jawabin bayan taron ya bayyana, tuni zauren Kakakin Majalisun Dokokin na jihohi ya kafa wani ingataccen kwamiti domin zama da kungiyar ma’aikatun majalisun da zummar shawo kan matsalolin nasu.

Taron na Bauchi ya kuma jinjina wa Gwamnan Jihar, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad bisa yadda gwamnatin sa ta karbi bakwancin shugabannin majalisun dokokin na jihohin tarayyar Nijeriya, iya tsawon badoncin su a garin Bauchi.

Daga nan, sun nuna damuwarsu matuka kan matsalolin tsaro da suke addabar kasar nan, inda suka yi kira da a dauki matakan da suka dace wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’ummomin kasar nan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Sha Alwashin Magance Kalubalen Da Kafar GMC Ke Fuskanta

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Nemi Da A Bai Wa Kwamitin Gyaran Mulkin Jam’iyyar Hadin Kai

RelatedPosts

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar dokar...

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

by Daurawa Daurawa
13 hours ago
0

Daga Rabi'u Ali Indabawa, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya,...

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

by Muhammad
16 hours ago
0

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira...

Next Post
Gwamnan Gombe Ya Nemi Da A Bai Wa Kwamitin Gyaran Mulkin Jam’iyyar Hadin Kai

Gwamnan Gombe Ya Nemi Da A Bai Wa Kwamitin Gyaran Mulkin Jam’iyyar Hadin Kai

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version