Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Makarantar Koyon Sana’ar Hannu Dake ‘Yankara Ta Yaye Dalibai Karo Na 11

by
1 year ago
in LABARAI
3 min read
Sana'ar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Abdullahi Sheme,

A makon da ya gaba tane makarantar koyar da sana”oin hannu ta garin ‘Yankara dake karamar hukumar Faskari a jihar Katsina ta kara yaye dalibanta karo na 11 a harabar makarantar a garin na ‘Yankara.  Tun da farko a nasa jawabin, shugaban makarantar Malam Galadima Dantsafe shi ne kuma Farin Ganin Sarkin Yamman Faskari ya yi dogon jawabi na tarihin kafa makarantar inda ya ce, yanzu sun yaye dalibai sama 120 tun kafuwar makarantar wani bawan Allah mai kishin mahaifarsa da al”ummar yanki ne ya kafa makarantar, mai suna njiniya Alhaji Shehu Sallau Yankara Wakilin Wajen Katsina, ya ci gaba da cewar yau  kimanin shekaru 11 kenan da fara koyawa mata sana”oin hannu sana”oin sun kunshi koyar da dinkin keke da koyar da sakar hannu da yin manshafawa da turaren kamshi na fesawa a dakuna da ruwan omon wanke wanke da koyar da gyaran gashi na mata da dai sauran sana’oi shugaban makarantar ya ci gaba da cewar wannan makarantar tana koyawa matan aure da ‘yammata da zawarawa musamman wadanda a ka kashe masu mazaje da ‘yan ta”adda suke yi a wannan yanki namu mai albarka duk abinda wannan makaranta take da shi na koyarwa kamar irinsu sinadiran da a ke hada sabulan wanka da wanki da na turaren kamshi da atamfofin da a ke yankawa don koyawa matan dinki da zaren dinki da duk abinda za a nema don yin aikin wanda ya kafa makarantar ya samar da su kyauta ya ce tuni ya sanya manyan kekunan dinki a wannan wurin koyar da sana”oin hannun Dantsafe ya ce, babu abinda za su cema wanda ya kafa wannan makarantar watau, Alhaji Shehu Sallau ‘Yankara Sarkin fadar ‘Yankara

Barayan Faskari kuma shi ne Wakilin wajen Katsina sai godiya da fatan alkhairi kuma Allah ya biyashi da mafificin lada irin wadannan bayin Allah a keso a cikin al”umma saboda taimakonsu daga nan ya mika godiyarshi ga wani bawan Allah Alhaji Abdulkadir Aliyu Faskari AK wanda ya taba  ba makarantar gudunmawar kekunan dinki guda 10 don a cigaba da koyama matan sana”oin ya ce wannan ba karamin abin a yabo bane daga nan ya yi kira da babbar murya ga masu hannu da shuni da manyan ‘yan boko da manyan manoman yankin su kawo gudunmawarsu don matan yankin su dogara da kansu a nashi jawabin wanda ya kafa makarantar Injiniya Alhaji Shehu Sallau ya ce kishin gida  da son ganin kowa ya tashi ya dogara da kanshi yasa ya kafa wannan makarantar don koyawa iyayenmu sana”a musamman mata domin sune suke dawainiya da gidajenmu da tarbiyar da yaranmu kuma ta haka ne za a magance tallar da kananan yara ‘yam mata ke yi wasu ta hanyar talla ne a ke yi masu fyade.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wakilin Wajen Katsina ya cigaba da cewar yana kishin mahaifarshi da jama”ar yankinsu kuma jama”a su tashi tsaye su dogara da kawunansu sannan ya yi kira ga yan boko da masu hannu da shuni su dawo gida su taimaki jama”a su yi koyi da mutane masu kishi ba a koma gefe guda a na surutai ba ya kara da cewar mu fito mu hada karfi da karfe don mu ciyar da al”ummar gaba daga karshe an raba kyaututtuka ga matan da suka yi kwazo wajen koyon sana”oin mutane da yawa suka yi jawabai a wurin yaye daliban kamar irinsu Alhaji Ali Musa ‘Yankara Danmasanin ‘Yankara da Malam Aminu. Mairuwa sannan a ka kaddamar da saida takardun cikewa na shiga makarantar karo na 12 an yi addi”oi na samun zaman lafiya a yanki da halartar manyan baki da yawa da suka zo daga wurare daban daban.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Aikin Samar Da Tsaro Na Kowa Da Kowa Ne -Alhaji Ibrahim Ado Abdullahi

Next Post

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Bayyana Alhinin Rashin Wakilin Muryar Amurka

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
6 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
8 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
19 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
Majalisar

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Bayyana Alhinin Rashin Wakilin Muryar Amurka

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: