Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Makon Mata Masu Ciki: Hafsat Ganduje Ta Jinjina Wa Mata A Kano

by Muhammad
December 24, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Masu ciki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka,

 

samndaads

Uwar Gidan Gwamnan Jihar Kano, Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje, ta kara tunatar da mata muhimmancin zuwa awon ciki da kuma kula da alluran riga-kafin da ake yi wa kananan yara.

Farfesa Hafsat Ganduje ta yi wannan tunatarwa ne a lokacin da ta ke kaddamar da makon duba lafiyar mata masu dauke da juna biyu da kananan yara wanda Gwamnatin Jihar Kano ta shirya karkashen Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano.

Ta kuma kara da kiran maza da su rika tausayawa matansu masu Juna biyu ta hanyar kulawa da ba su abinci mai gina jiki da kara lafiya.

Bayan nan ta raba kyaututtuka da kayan abinci masu gina jiki ga matan da suka zo asibitin, domin yin awo da kawo yara rigakafi.

A nasa jawabin, Kwamishinan Lafiya, Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa, ya ce kasancewar cutar kyanda na saurin hallaka kananan yara ya sa Ma aikatar Lafiya ta Kasa ta mayar da yin rigakafi sau biyu ga kowane yaro a wata.

Dakta Tsanyawa ya kuma ce Ma’aikatar Lafiya za ta ci gaba da yaki da cutar tarin fuka da cutar yunwa da kuma cutar corona da dukkan cutar da ke saurin yaduwa a tsakanin al’ummah.

A nasa bangaren, mai Martaba Sarkin Rano, Alhaji Kabiru Muhammad Inuwa, ya yi karin haske ne bisa yadda ake karbar alluran a garin Rano tare da yin kira ga mata masu juna biyu da su mayar da hankali wajen cin abinci da zai kara lafiyar su da abinda su ke dauke da shi acikinsu su kuma rika zuwa awon ciki. Kamar yadda Jami’ar yada labaran Ma’aikatar lafiya Hadiza Mustapha Namadi ta shaida wa LEADERSHIP A Yau.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kotu Ta Bada Umarnin Kamo Mahadi Shehu Bisa Kin Halarta Kotu

Next Post

Korona: Buhari Ya Tsawaita Ayyukan Kwamitin Kar-ta-kwana Kan Yaki Da Korona

RelatedPosts

Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Boko Haram A Borno 

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Rundunar sojan Najeriya ta bayyana samun nasarar tarwatsa sansanin da...

Jam'iyyar Adawa

Jam’iyyar Adawa Ta PDP Ta Yi Babban Kamu A Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kebbi tayi babban kamu...

Majalisar Malamai

Majalisar Malamai A Kogi Ta Raba Zakkar Miliyan N2.5 Ga Mutum 63

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Majalisar Malamai ta Najeriya,reshen jihar Kogi(Council of Ulama) ta rarraba...

Next Post
'Yan Nijeriya

Korona: Buhari Ya Tsawaita Ayyukan Kwamitin Kar-ta-kwana Kan Yaki Da Korona

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version